Iyalan ‘yar wasan Nijeriya da aka sace sun koka yayin da ‘yan bindiga suka nemi fansa

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Iyalan ‘yar wasan ƙwallon ƙafa ta Nijeriya, Ihotu John Rebecca, sun roƙi ‘yan ƙasa da su gaggauta kawo musu ɗauki sakamakon sace ta da aka yi a babban titin Benin.

‘Yan bindigar da suka yi garkuwa da ita sun nemi a biya fansar Naira miliyan 20 a matsayin kuɗin fansa.

Rebecca matashiyar ‘yar wasa ce da ke buga wa ƙungiyar Pecesetter Queens FC a Gasar Premiership ta Nijeriya ta mata, wato NWFL, wadda aka yi awon-gaba da ita a lokacin da take kan hanyar koma wa gida.

Iyalan nata sun bayyana ta a matsayin ɗaya daga cikin ‘yan wasan da ke bayar da gagarumar gudunmawa ga harkokin ƙwallon ƙafa na mata a Nijeriya.

A cewarsu, “Muna roƙon masu ruwa da tsaki a harkokin ƙwallon ƙafa, jagororin ƙungiya, masu ɗaukar nauyi, jami’an gwamnati, masu kula da wasanni da dukkan wani ɗan ƙasa da zai iya taimakawa.”

A yanzu dai hukumomi ba su tabbatar da al’amarin ba, yayin da ake ƙoƙari wajen ganin an sako ta.

By Babaji