Lasisin shigo da man biliyan N100 na Dangote: Kotu ta yi fatali da ƙarar NNPC

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Alƙali Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja, ya yi fatali da ƙarar Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), ta ƙalubalantar takardar lasisin shigo da man fetur na Naira Biliyan 100 na matatar man Dangote.

A hukuncin da ya yanke, Alƙali Ekwo ya ce hukumar ta NNPC ta gaza gabatar da ƙara irin wadda matatar man Dangote ta shigar a gaban kotu, saɓanin dokokin da suka dace a shari’ar kotu.

Alƙalin ya ƙara da cewa, inda aka taɓo batun shari’a, kotu na iya magance ta a lokacin da za ta yanke hukunci.

Ya zargi hukumar NNPCL da saɓa doka ta 16 na babbar kotun tarayya ta hanyar shigar da ƙara da ba ta dace ba a kan matatar.

Mai shari’a Ekwo ya ci gaba da cewa, NNPC ba zai fuskanci rashin adalci ba idan matatar Dangote ta gyara mata ƙara.

Dangane da buƙatar matatar Dangote na gyara ƙarar ta don bayyana sunan hukumar ta NNPC yadda ya kamata, Mai shari’a Ekwo ya ce dokar gyaran matatar ta ba da dama.

Daga nan sai ya amince da gyara matatar man sannan ya ce NNPC na da ƙarar da za ta amsa.

By ukarofi