
Daga BELLO A. BABAJI
A safiyar ranar Laraba ne Mahaifiyar Gwamnan Jihar Jigawa (Umar Namadi), Hajiya Maryam Namadi ta rasu.
Sakataren Labaran gwamnan, Hamisu Mohammed Gumel ya faɗi hakan a wata sanarwa da ya fitar.
Ya ce za a gudanar jana’izarta ne a yammacin ranar kamar yadda addinin musulunci ya tanadar a garin Kafin Hausa.
Gwamnan da iyalansa sun buƙaci al’umma da su sanya ta a cikin addu’o’insu don samun rahamar Allah SWT.
