
Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ba za ta amince da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC) na jam’iyyar PDP da Kabiru Turaki ke jagoranta ba, saboda hukuncin kotuna da har yanzu suke aiki da kuma shari’o’in da ba a kammala ba.
INEC ta ce ta karɓi buƙatu daga lauyoyin PDP na neman a amince da shugabannin ƙasa da aka ce an zaɓa a Babban Taron Jam’iyyar da aka gudanar a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025, a Ibadan, Jihar Oyo. Sai dai bayan duba buƙatun, hukumar ta yanke shawarar ƙin amincewa da su bisa doka da hukuncin kotuna.
Hukumar ta nuna cewa, akwai hukunci biyu na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja da suka hana ta kulawa, sa ido, ko amincewa da sakamakon taron jam’iyyar PDP, har sai an cika umarnin kotu gaba ɗaya. INEC ta jaddada cewa duk da an shigar da ƙorafe-ƙorafen ƙara, ƙara ba ya hana aiwatar da hukuncin kotu.
INEC ta ƙara da cewa akwai wata shari’a da PDP ta shigar a Babbar Kotun Tarayya da ke Ibadan wadda har yanzu tana gaban kotu. Don haka, hukumar ta ce ba za ta iya amincewa da buƙatar PDP ba har sai an kammala dukkan shari’o’in.
INEC ta tabbatar wa jama’a cewa za ta ci gaba da bin doka, kundin tsarin mulki, da kuma mutunta hukuncin kotuna a dukkan harkokinta.
