*Tinubu ya amince da rangwamen haraji ga gidajen jarida
*Gwamnatin Tarayya ba ta tsangwamar manema labarai, inji Idris
Daga SANI AHMAD GIWA da MAHDI MUSA MUH’D
Shugaban ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE), Kwamred Eze Anaba, ya koka kan yadda tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki suke hana kafafen yaɗa labarai gudanar da aikinsu yadda ya kamata, yana mai roƙon Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakan tallafi, don ceto masana’antar da ke fuskantar barazanar rushewa.
Yayin da yake jawabi a taron shekara-shekara na 21 na ƙungiyar Editoci ta Nijeriya (ANEC), wanda aka gudanar a Dakin Taron Fadar Shugaban ƙasa a Abuja, Anaba ya bayyana cewa halin tattalin arzikin ƙasar na barazana ga ɗorewar kafafen watsa labarai.
“Yawancin jaridu da gidajen talabijin a yau ba sa iya biyan albashin ma’aikatansu — ba wai saboda rashin ƙwarewa ba, sai dai saboda tsadar samar da abun bugawa da kayan aiki. Misali, jarida ɗaya na iya kashe har sama da naira miliyan 1.3 zuwa 1.4 a wata wajen sayen tawada da faranti da ake shigowa da su daga ƙasashen waje,” inji shi.
Ya ce, idan ba a tabbatar da ɗorewar tattalin arzikin kafafen yaɗa labarai ba, to aikin da kundin tsarin mulki ya ɗora musu — na wayar da kai da kuma riƙe gwamnati da alhakin aikinta — yana cikin haɗari.
Anaba ya yi kira kai tsaye ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya ɗauki mataki, “Gwamnatinka tana ƙoƙari wajen samar da ayyukan yi, amma idan kafafen labarai ba za su iya biyan ma’aikatansu ba, ba za su iya tallafa wa demokiraɗiyya ba. Shi ya sa muke neman agajinka, Mai Girma Shugaba, don ƙarfafa masana’antar labarai.”
Shugaban NGE ya buƙaci gwamnati ta kafa tsarin tallafi na musamman kamar yadda ake yi a ƙasashe irin su Kanada, Indiya da Afirka ta Kudu — ciki har da tallafin kuɗi, rage haraji, da rance mai ƙarancin ruwa don tallafawa kafafen yaɗa labarai.
Ya kuma buƙaci a kafa tallafin ci gaban dijital da sabunta kayan aiki, wanda zai taimaka wa kafafen labarai su ƙara ƙwarewa wajen watsa sahihan bayanai, gudanar da ingantaccen ruwaito kan zaɓe, da tallafawa ci gaban al’umma a yankunan karkara.
Bugu da ƙari, Anaba ya nemi kafa tsarin rance mai sauƙi da zai ba kafafen labarai damar gudanar da ayyukansu ba tare da nauyin bashi mai tsanani ba.
“Muna roƙon gwamnatin ku da sauran matakan gwamnati da su ba da damar samun kuɗaɗe masu sauƙi domin ɗorewar kafafen yaɗa labarai,” inji shi. “Ya zama wajibi a kafa tallafin dijital wanda zai faɗaɗa isar da labarai, ƙara ayyukan yi, kuma ya kare dimokiraɗiyya.”
Anaba ya jaddada cewa idan ba a ɗauki irin waɗannan matakai ba, kafafen yaɗa labarai na iya gaza cika rawar da suke takawa wajen haɗa ƙasa da sanar da jama’a.
Ya kuma bayyana cewa a lokacin da ake fama da matsin tattalin arziki, rashin tsaro, yaɗuwar ƙarya da ƙarancin amincewa da gwamnati, editoci suna da rawar gani a matsayin masu kare gaskiya da tabbatar da gaskatattun bayanai.
Sai dai kuma, a wani ci gaban kuma, Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da buƙatun da ƙungiyar Editoci ta Nijeriya (NGE) ta gabatar don ceto kafafen yaɗa labarai daga matsin tattalin arziki, ciki har da rangwamen haraji, cire harajin ɓAT, da damar samun lamuni mai sauƙi, domin farfaɗo da ayyukan kafafen labarai a ƙasar.
Shugaban ƙasan ya bayyana hakan ne a yayin buɗe taron shekara-shekara na 21st All Nigeria Editors Conference (ANEC) da aka gudanar a Fadar Shugaban ƙasa, Abuja, ranar Laraba.
Ya ce, ya karɓi cikakken bayani daga shugabannin NGE game da buƙatar kafafen yaɗa labarai, inda suka nemi gwamnati ta ba su rangwamen harajin kamfanoni na tsawon shekaru 10, ƙarin lokaci kafin biyan ɓAT, da damar samun rance mai rahusa daga Bankin Masana’antu (BOI) da kuma tallafin ci gaban fasahar dijital.
“Na saurari buƙatunku – rangwamen haraji, ƙarin lokaci a ɓAT, lamuni mai sauƙi, da tallafin dijital. Ku sani, ni a matsayina na shugaban ku, na amince da buƙatunku. A ma’anar gaskiya, ina da su a cikin aljihuna,” inji Tinubu cikin dariya.
Shugaban ƙasan ya yaba da rawar da kafafen yaɗa labarai suka taka tun kafin samun ‘yancin kai, yana mai gargadin cewa yaɗa bayanai ba tare da tantance gaskiya ba da yin ƙiyayya ko nuna son zuciya na iya zama barazana ga haɗin kan ƙasa.
“Ƙarfinku a matsayin editoci ya dogara ne kan gaskiya, basira, da kishin ƙasa. Jaridu da kafafen yaɗa labarai suna da rawar da za su taka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsare dimokuraɗiyya,” inji shi.
Tinubu ya bayyana cewa lafiyar dimokuraɗiyyar ƙasa tana da alaƙa kai tsaye da aikin jarida mai gaskiya, ba kawai zabe ko doka ba. Ya ce kafafen yaɗa labarai dole su kasance tushe na gaskiya, haɗin kai, da riƙon amana, musamman a wannan lokaci da ƙaryar yanar gizo da rashin amincewar jama’a ke ƙaruwa.
Shugaban ƙasan ya jinjinawa ƙungiyar NGE saboda ci gaba da shirya tattaunawa kan ƙa’idojin aikin jarida da ƙarfafa dimokuraɗiyya, yana mai cewa hakan na nuna muhimmancin kafafen yaɗa labarai wajen tsara alƙiblar ƙasa.
“Jarida a Nijeriya ta kasance kayan faɗakarwa da ya tsaya daram a lokutan rikici. Ina girmama jaruman ‘yan jarida da suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare gaskiya da adalci,” inji Tinubu.
Bugu da ƙari, a wani labarin kuma, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce jajircewar Shugaba Bola Tinubu ga ’yancin manema labarai yana da matuƙar muhimmanci ga hangen nesansa na samun cigaba a Nijeriya.
Ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Laraba a taron ƙungiyar Editocin Nijeriya, yana mai jaddada cewa, babu wata kafar yaɗa labarai da ake yi wa barazana ko aka rufe a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.
“Babban abin da ke cikin wannan hangen nesa na ci gaban Nijeriya shi ne yanayi inda ‘yancin fadin albarkacin baki da kafofin watsa labarai masu karfi za su iya bunƙasa. Ina tsaye a gabanku a yau don tabbatar da cewa a karkashin jagorancin Shugaba Tinubu, mun bunkasa tsarin kafofin watsa labarai mai daidaito wanda ba a taba ganin irinsa ba,” inji Idris.
“Tare da gidajen rediyo da talabijin masu lasisi sama da 1,000 da ke aiki a faɗin ƙasar, yana da mahimmanci a lura cewa babu ɗaya daga cikin waɗanda gwamnati ta yi barazana, ta yi musu ba’a, ko kuma ta dakatar da su saboda nuna rashin amincewarsu.
“Wannan ba wani abu bane da ya faru kwatsam, amma an yi shi ne bisa ga ƙa’idodin kundin tsarin mulki na ‘yancin manema labarai,” inji shi.
Ministan ya bayyana cewa an amince da jajircewar Tinubu ga ‘yancin manema labarai a duk duniya, wanda hakan ya sa aka bai wa gundumar damar ɗaukar nauyin Cibiyar Kafafen Yaɗa Labarai ta Duniya da Karatu da Bayanai.
A cewarsa, babban taron zai haɗa Nijeriya da yanayin da kafofin yaɗa labarai ke ciki daga ko’ina cikin duniya, tare da Ma’aikatarsa a shirye take ta yi amfani da wannan dandamali don nuna ci gaban ƙasarmu.
“Muna hanzarta canza tsarin bayananmu don ƙara wannan, tare da tabbatar da cewa ba wai kawai muna amfani da bayanai ba, har ma muna jagorantar ƙirƙirar yanayin kafofin yaɗa labarai na duniya masu ilimi, fahimta, da kuma ɗabi’a,” inji ministan.
Ya yi kira ga editocin da suka taru a taron da su ga kansu a matsayin abokan hulɗa masu muhimmanci a sabunta ƙasa.
“Gwamnatin Shugaba Tinubu ta nuna imaninta a gare ku ta hanyar ayyukanta, ba kawai maganganunta ba. Muna gayyatarku da ku shiga tsakani, ku yi sharhi mai kyau, kuma ku bayar da rahoto tare da alhakin da wannan lokaci a tarihinmu ke buƙata.
“Bari mu yi aiki tare don ba da labarin Najeriya cikin daidaito, da gaskiya, da kuma imani mai ƙarfi ga alƙawarin babbar ƙasarmu,” inji shi.
A cewarsa, Tinubu ya fahimci cewa kafofin yaɗa labarai masu ƙarfi, masu zaman kansu ba abokan hamayyar gwamnati ba ne, amma ginshiƙin da ake gina dimokuraɗiyya ta gaskiya da ɗorewa a kai.
