Yin amfani da marubuta zai iya shawo kan matsalar tsaro a Nijeriya – Malumman Matazu

Spread the love

 “Da Rana tsaka na tsinci kaina a matsayin marubucin waƙa”

Daga AISHA ASAS

Abdulhamid Muhammad Sani wanda yawanci suka fi sani da Namatazu ko Maluman Matazu, marubuci wanda ya yi fice kuma ya shahara wajen rubutawa da tsara rubutacciyar waƙa. Shi dai mazaunin garin Matazu da ke Jihar Katsina. A wannan hirar da Aisha Asas ta yi da shi ya taɓo batutuwa da dama da suka shafi rayuwar sa, ƙalubale da kuma irin gudunmuwar da marubuta ke bada wa ga al’umma. Ga dai yadda hirar tasu ta kasance:

MANHAJA: Masu karatu za su so jin taƙaitaccen tarihinka?

NA MATAZU: Bismillahir Rahmanir Raheem. Da farko dai sunana Abdulhamid, ni ɗa ne ga Liman Muh’d Sani, Muh’d, Sani kuma ɗa ne ga marigayi Liman Malam Bala, Babban limamin Matazu. An haife ni a Unguwar ƙofar Gabas garin Matazu, ƙaramar Hukumar Matazu Jihar Katsina. Na fara karatun allo wurin mahaifina tun ina ɗan mitsitsi, bayan na tasa na shiga makarantar Matazu Model Furamare. Bayan kammalawa duk da cewa na yi nasarar cin jarrabawar mashahuriyar makarantar nan da ke Katsina wato ATC, amma aka ɗauke ni zuwa makarantar Allo a garin Bauchi. Bayan Bauchi na kuma ziyarci wasu garuruwan don ƙara faɗaɗa karatun ƙur’anin. Daga baya na dawo na tare Bauci, in da na kama sana’ar siyar da littattafai na kuma zama babban jami’in da ke yaɗa Jaridar Attatbiƙ a jihohin Arewa maso-gabas amma ban da jihar Borno. Na kuma tsunduma neman ilmin addini a zaurukan malamai, tare da shiga makarantar: Bauchi Institute for Arabic and Islamic Studies Inda na fara karatun shaidar mataki na biyu, ban kai ga kammalawa ba na yii aure, da kamalawa ta kuma na yi NCE kan ilimin addinin musulunci da harshen larabci. Kammalawa ta ke da wuya mahaifi na ya rasu, hakan ya sa na dawo gida Matazu, inda na fara aiki a makaranta mai suna: “Matazu integrated learning Academy” MILA a taƙaice. Yanzu haka kuma ina aiki a Matazu Mode Furamare tare da Makarantun Islamiyyu biyu da na ƙirƙira da kai na a garin mu na Matazu, kuma har yanzu ina cigaba da karatu.

Ya a ka yi ka samu kanka a fagen marubuta?

Tun tasowa ta na kasance mai matuƙar sha’awar karatu da rubutu, tun ina gida tare da abokan karatun allo na, na kasance cikin na gaba-gaba wajen yawan yin rubutun ajami, don isar da duk saƙon da na ke son isarwa, uwa uba kuma shiga ta Furamare sai himmar son karatun ta daɗu, musamman ma da ya ke boko ta fi yaɗuwa tsakanin kowa da kowa.Tun ban kammala Furamare ba na naƙalci karantawa ‘yan’uwa na yara littattafan tarihi da yaƙe-yaƙe, misalin irin littafin Tarihin Annabi Kammalalle na Alhaji Abubakar Imam da Shehu Umar wallafar Alhaji Abubakar Tafawa ɓalewa da makamantan su. Don haka lokacin da girma ya zo sai na zurfafa sosai kan rubutun. Hakan ne ya sa har na zama mai tura rahotanni ga wasu jaridu da kuma yin sharhi kan al’amurran yau da kullum. Sai dai duk lokacin ban fara rubutun rubutattar waƙa ba tukunna. Amma sanadin fara rubutun waƙa, ya samo asali ne lokacin babban rashin da yankin mu ya yi na Malam Musa ɗan’azumi, wani mutum ne jigo da ya yi matuƙar bayar da gudunmuwa don cigaban ilmi a yankin na mu. Sai na ga tun kan gwamnati ta samar da wani abu, na tunawa da shi ni ma ya kamata na yi wani abu na tunawa da shi ɗin. Haƙiƙa ƙirƙirar waƙar ta’aziyyar ita ta buɗe min sabon babi na rubuce-rubuce.

Daga nan na jajirce wajen samar da wasu waƙoƙin kan jigogi daban-daban, misali na yi a kan ɗumunci, ilimi, lokaci da kuma tashin ƙiyama sai kuma ta firgici da ke bayanin halin da Arewa ta faɗa a lokacin tashin bamai-bamai da satar ‘yan mata, na rerata a taron cika shekara na Makarantar Malam Bambadiya ta Farfesa Ibrahim Malumfashi da akai taron a Jami’ar Jihar Kadun. Jul 25, 2018.

Sunanka ya shahara sosai a cikin marubuta musamman masu tu’ammuli da kafar sadarwa ta zamani. To shin menene sirrin?

Tun lokacin da na ƙyalla ido na ga ɗimbin alfanun da ke tattare da kafar sadarwa ta Fesbuk (da yake ita na fara sani), sai na tsaya na ga tabbas ina da hajar da zan baza ni ma a wannan babbar kasuwa mai cike da jama’a. Aka kuwa yi sa’a sai na bazama amfani da ita wurjanjan, na kasance in ina da wani tunani kyakkyawa sai na rubuta, cikin ikon Allah kuwa in ga masu tsokaci na yi, duk da cewa wasu ‘yan uwan kan yi suka. Amma wasu da dama ƙarfafa min gwiwa su ke yi. Sai ya zama masu sukar ma nakan ɗauke su a masoya na kusa, wannan kuma ban ɗauke shi yin kai na ba, a’a yin Allah ne.

Wacce shekara ka tsunduma a duniyar rubutu?

A shekarar 2013 lokacin ban jima da fara amfani da kafar sadarwa ta yanar gizo ba, sai ga sanarwar yanke cibiyar ƙungiyar Marubutan Jihar Katsina (KMK) da aka yaɗa sanarwar taron a Katsina, ganin sanarwar da na yi sai na niƙi-gari daga Matazu zuwa birnin na Dikko musamman don halartar wannan taro. A wannan ranar ne na yi ido da ido da ɗimbin marubutan da ban taɓa ganin su ba, sai dai jin muryoyinsu a rediyo ko karanta littattafansu ko rubutunsu a jaridu. Har aka ban dama na rera waƙar da na rubuta kan muhimmancin ribatar lokaci.

Kasancewar ka sananne cikin marubuta wanda ya karkata ga rubutattun waƙoƙi. Shin ya rubutun zube shi ma ana taɓawa?

Ko shakka babu na fi karkata ga rubutattar waƙa, to amma duk da haka ban zauna ba kan ita kaɗai, domin kuwa na rubuta littafin tarihin Annabi (SAW) da ajami da na raɗa wa suna: ‘Babban Masoyi Annabi Muhammadu (SAW). Littafi ne da na rubuta don koyarwa a makarantun Islamiyyu musamman waɗanda suke yankunan karkara. Bayan shi akwai wani mai suna ‘Ki Kula da Tsarkin Ki’ shi kuma na bayani ne akan mas’alolin jinanen al’adar mata da hukunce-hukuncen wanka da tsarki na ibada. Dukkan su yanzu haka ana kan aikin buga su, bayan su ma akwai wasu da yanzu haka nake aikin rubuta su.

A cikin waƙoƙinka wacce ce bakandamiyar ka?

Duk waƙar da na rubuta ina jin kamar ta fi kowace in ina nazarin ta, to amma gaskiya waƙar da na rubuta ga shugaban dukkan halittu, mai baitoci dubu na yabo da tarihin Manzon Rahama da na ke kira da ‘Alfiyya’, ban jin zuwa yanzu ina da waƙa mai yawa mai kuma fa’ida kamar ta, don haka ita ce bakandamiya ta.

Me ya ja hankalinka har ka rubuta wannan waƙa sha kundum haka?

Babban abin da ya ja hankali na ga rubuta ta shi ne; don nuna soyayya ta da ƙauna ga fiyayyen talikai (SAW) burina ni ma na bayar da gudunmuwa ta ga al’umma wajen ƙara ƙauna da sallamawa ga Manzon mu Annabi Muhammadu (SAW)

Wane lokaci ka fi jin daɗin rubutu?

A dukkan lokaci in dai na samu dama, nakan ji daɗin rubutu, sai dai ɓacin rai ko wata damuwa kan hana ni sukunin iya yin rubutu, don haka duk lokacin da nake cikin irin wannan hali nakan ƙaurace wa rubutu. Kuma ban son ƙara ko hayaniya a a lokacin da nake rubutu.

Me ke faranta maka rai me kuma yake baƙan ta maka rai?

Babban abin da ke faranta min rai shi ne yunƙurin da na yi kuma na yi nasara, na assasa makarantar Madrasatul Tarbiyyatil Ummatil Islamiyya, a garin mu na Matazu.

Wacce nasara ka samu a fagen waƙoƙinka da rubuce-rubuce?

Babbar nasarar da na samu ita ce; duk da cewa waɗanda suka sanni sukan ba da shaida akai na kan cewa ina aiki tuƙuru, wajen karantarwa ga al’ummar da na ke ciki, tare da wayar da kai, to sai dai manyan iyayen ƙasar yanki na sun sanni cikakken sani, ta sanadiyyar rubutu. Bayan wannan kuma ga fara kwararowar ɗalibai daga jami’o’i da suke nazarin waƙoƙi na, tare da ƙara sanayya da manyan malaman jami’a duk ta sanadin rubuce-rubucen na samu wannan gagarumar nasarori.

Wane ƙalubale babba ka taɓa fuskanta sanadiyyar rubutu?

Wani rubutu da na yi akan wani al’amari da ya faru a wani birni a nan Arewa, wani abin mamaki da yawan masu sharhin al’amurran yau da kullum in ma a jaridu ko a rediyo, dama wasu manyan mutane duk sun tabbatar da gaskiyar lamarin kan ra’ayin da ni ma na rubuta. To amma nawa ra’ayin kan mas’alar sai ya jaza min mummunar fahimta da wasu al’ummomi da na ke huɗɗa da su, ba maganar fatar baki kawai suka tsaya ba, har sai da ta kai suka ban takardar kora, a wasu wuraren su da na ke samun taro sisi don kula da kaina. Wannan dambarwa ta sabbaba na rubuta wata waƙa da na sanya wa suna ‘ɗanyen Hukunci’, inda na yi cikakken bayanin lamarin tare da fin ƙarfin da aka gwada min. Yanzu haka waƙar na nan na taskace don nazari ga ‘yan baya, kan illar yanke hukunci ba tare cikakken bincike ba. Musamman ma ni da yake ba a je ko’ina ba sai da gaskiya ta yi halin ta. Wannan ne babban ƙalubalen da ba zan taɓa mantawa da shi ba a harka ta ta rubutu.

A cikin marubuta, mawaƙa da mashawarta waɗanne ne gwanayenka?

Gwanaye na a rubutattar waƙa akwai: Dr. Aliyu Aƙilu, Dr. Aliyu Namangi Zariya, Alhaji Aminu Abubakar Ladan (Alan waƙa). A marubuta kuwa akwai: Alhaji Abubakar Imam, Shaikh Nasiru Kabara, Malama Asma’u bint Fodiyo. Gwanaye na a fannin shawara kuwa akwai: Malam Nasiru Ahali, Malam Murtala Faggo, da sauransu da dama.

Kana da malamai ko ubangida a harkar rubutun waƙa?

Da rana tsaka na fara rubuta waƙa, don haka na samar da waƙoƙi da dama ba tare da wani ne malami na kan waƙar ba, sai dai daga baya duk da yadda mabiyan ayyuka nake koɗa ni akan gwanance, ban aminta da ikirarin su ba, sai ma na nemi ɗauki wajen wata marubuciya a Kaduna mai suna Aunty Sadiya Kaduna in da ta yi min jagorar sada ni da fitaccen masanin rubutattun waƙoƙin nan da ke Kano wato Malam Nasir G. Ahmad ‘Yan awaki, inda Malam ya karɓe ni hannu biyu, ya duba min waƙoƙi na guda huɗu, ya kuma sanya ni a hanya miƙaƙƙa kan rubutattar waƙa. ƙari kuma kan hakan sai na zama ɗaya cikin ɗaliban Farfesa Ibrahim Malumfashi na makarantar da yake jagoranta a yanar gizo da ake koya gundarin adabin Malam Bahaushe. Don haka Malam Nasir G. Ahmad da Farfesa Ibrahim Malumfashi su ne malamaina a rubutacciyar waƙa.

Ka taɓa rera waƙa a sutudiyo?

Sau ɗaya na taɓa zuwa sutudiyo na ‘yan kasuwa inda na rera waƙata ta lokaci, daga nan ban ƙara zuwa ba, sai in na je gidan rediyo sukan nemi na je don su tace don su riƙa sanyawa ga al’umma don amfana gaba ɗaya. Kuma duk waƙoƙina da aka tace a sutudiyo ba ko guda ɗaya da akai amfani da kayan kiɗa na zamani ko na garggajiya, waƙoƙin ne kaɗai ake tacewa, don ni ban sha’awar amfani da kayan kiɗan kowane kala, don waƙoƙina ba don zamani nake rubutawa ba, ba kuma don in samu kuɗi ba, ina yi ne don faɗakarwa, wa’azantarwa, Ilmantarwa da makamantan waɗannan.

Wacce waƙa ce ka fi shan gwagwagwa wajen rubuta ta?

Waƙa ta mai suna ‘Gagara Gwari’, wadda na rubuta musamman don in rera a taron Makon Hausa da aka shirya a 2015 a Jami’ar Ummaru Musa ‘Yar’aduwa da ke Katsina, waƙa ce da na ke kirara harshen mu na Hausa da ƙara fito da fifikon sa, to amma da na tura da wasu ‘yan baituka a farfajiya ta ta Fesbuk sai wani ɗalibi mai digri na biyu a harshen Hausa a lokacin kuma mai matuƙar ban shawarwari kan ayyukan adabi na wato Malam Jibril Yusuf sai ya ƙalubance ni akan cewa; ya kamata aji luguden harshe a waƙar, ma’ana ta zama mai sassarƙa kalmomi masu wahala da samar da tsofaffin kalmomi masu wuyar gane ma’ana, wannan ƙalubale da ya yi min sai ya sa na ƙara azamar inganta waƙar, sai ma kuma na ƙara da wasu abubuwan da sai daga baya na hararo su. 

Ya batun waƙoƙin zamani irin na fim da kuma hip-hop?

A gani na kowace irin waƙa mai ma’ana za a iya amfani da ita don yin fim, don ni yadda na ɗauki fim wani abu ne da ke koyar da kyakkyawa da gujewa munanan abubuwa marasa alfanu. Duk da yake dai zamani ya zo da mafi akasarin fim ɗin da ake shiryawa shirme ne da tallar tsiraici. Waƙoƙin Hip-hop kuwa ni yadda na ɗauke su, waƙoƙi ne na yara ƙanana masu ƙuruciya ainun, don da yawa ni nakan rasa hikimar da ke cikin irin waɗannan waƙoƙin na hip-hop, kiɗa da tsalle-tsalle sun fi yawa a waɗannan waƙoƙi, don haka ni ban saka su cikin waƙoƙin fasaha ko ɗaya, illa dai ina ɗaukar su ‘yan zamani kuma wani zamanin zai zo da za a neme su a rasa gaba ɗaya.

Ka taɓa shiga gasar rubutacciyar waƙa?

A shekarar 2014 ƙungiyar marubuta ta Alƙalam da ke da cibiya a Kaduna, ta sanya gasar rubutacciyar waƙa a shafin ta na yanar gizo, cikin ɗimbin sha’iran da suka fafata na zama zakara a gasar. Haka kuma a 2016 na yi zama cikin zakarun gasar da ƙungiyar Phoets in Nigeria reshen Jihar Kano in da ta saka gasar kan jimamin cika shekaru 3 da rasuwar Sarkin Kano, Dr. Ado Bayero da taya sabon Sarki Muhammadu Sanusi na biyu murnar cika shekaru 3 kan karaga mulkin Kano. An yi bikin ba mu kyautuka a ɗakin taro na Amerikan Corner da ke babban ɗakin karatu na Janaral Murtala Muh’d da ke Kano. Bayan waɗannan na shiga wasu ƙananan gasanni in da na yi zakara. 

Zuwa yanzu ka taɓa samun lambobin yabo sanadin rubutun zube da na waƙoƙi?

ƙungiyar Duniyar Marubuta (DM) da ke da hedikwata a Kano ta karrama ni ta ban rubutattar takardar yabo kan aikin adabi na, haka nan ƙungiyar marubutan Jihar Katsina (KMK) ta taɓa karrama ni a ɗakin taro na jami’ar Ummaru Musa ‘Yar’adua da ke Katsina, bayan waɗannan ƙungiyoyi akwai wasu ma ɗaiɗaiku da suka karrama ni. Sai dai karramawar da tafi jan hankali na da kuma dukkan masoya na ita ce: Takardar da Fadar Maigirma Fagacin Katsina hakimin Matazu Alhaji Iro Maikano ta rubuto mini inda ta wanke ni daga rubutun da na bayyana maki a baya wanda wasu ba’adin mutanen yankin mu suka yi min mummunar fassara, har hakan ya sa suka yi min sanadin kora daga aiki, amma bayan ƙwaƙƙwaran bincike sai aka gano ƙullalliya ce aka shirya min. Hakan ya sa fadar ta ban rubutacciyar takarda inda ta wanke ni fes, wannan dambarwa ta sabbaba na rubuta waƙar da na rubuta mai suna: “ɗanyen Hukunci” Wannan takarda da Fadar Maigirma Fagaci ta ban ita ta buɗe min sabon shafi na rayuwa daga tsangwama sai na fara zama abin so hatta ga waɗancan mutane.

Kasancewar ka magidanci, uba, malamin makaranta uwa uba kuma ɗaya cikin jagororin al’umma waɗanne hanyoyi ka ke ganin za a bi wajen ƙara inganta tarbiyyar yaran mu masu tasowa da zamantakewar iyali mai inganci?

Kasancewar mu akasari al’ummar Musulmi dole in dai muna son inganta tarbiyyar ‘ya’yanmu to mu yi amfani da hadisin Fiyayyen halitta (SAW) da ya ke cewa “Ku ladabtar da ‘ya’yanku kan abubuwa uku, son Annabin ku, son iyalan Annabin ku da karatun Al’ƙur’ani. Ba shakka mu ka riƙe wannan bilhaƙƙi zamu kuɓuta daga matsalolin da suka addabe mu. ɓangaren zamantakewar iyali ma mu jarraba wannan, sannan mu ƙara sanin nauyin da ke wuyan mu, musamman mu iyaye maza, don maza mu ne shugabanni, kuma ya zama wajibi a nemi sana’a don ciyar da iyali da halal, cin haram ga iyalanmu babbar matsala ce da ke kawo cikas ga kowace irin al’umma.

Wane irin kallo ka ke yi wa marubuta?

Ina kallon marubuci ko marubuciya a matsayin ɗanbaiwa, mai hazaƙa, mai zalaƙa, jajirtacce, mai ɗimbin basira, wanda ke fitar da al’umma daga duhu zuwa ga haske, daga rami zuwa tudu daga ƙunci zuwa walwala, ƙari kan hakan Marubuta wayayyu ne, faɗakakku. Sai dai kuma duk kyan abu baka rasa baragurbi, lallai a marubuta akwai waɗanda ke amfani da baiwarsu wajen cutar da al’umma, don haka kirana gare su shine: su shiga taitayinsu, su dawo hanya don yin abinda ya dace don cigabantar da al’ummarsu.

Wacce rawa ka ke ganin marubutan zube da waƙoƙi za su iya takawa don daƙile yaɗuwar garkuwa da mutane, satar shanu da rikice-rikicen fulani da makiyaya da ya addabi wannan yanki namu?

Kamar yadda na ce miki a baya marubuta ‘yan baiwa ne, ba na shakkar cewa da ace hukumomi za su yi kyakkyawar kulawa ga marubuta akan a ummarce su su samar da hanyar daƙile matsalolin nan, da ba za a ɗauki wani lokaci za su samo bakin zaren. To amma shagulatin ɓangaro da hukumomi suka yi, da masu aikin ƙirƙira irin marubuta da makamantansu, na cikin dalilan da yasa aka kai inda ake yanzu ga lalacewar al’amura. Don haka kirana ga hukumomi su dawo kan bayar da duk tallafin da ya dace, don marubuta su samu damar kyakkyawan tunanin da za su rubuta, don hukumomi sui nazarin su don samun mafita, kan abubuwan da ya same mu na matsaloli.

To madalla mene ne fatan ka na ƙarshe?

Na jima ina so in samu damar miƙa jinjina ga wannan jarida ta Manhaja. Sannan ina godiya da jarida ta harshen Hausa da ta ke fitowa ko wacce juma’a wato Blueprint Manhaja da ake bugawa Abuja. Allah ya ƙara haɓaka mana ita da dukkan ma’aikatan ta.Wassalamu alaikum

To mun gode.

Ni ma na gode ƙwarai.

By ukarofi