Masu hannu da shuni su rinƙa tallafa wa mabuƙata a Ramadan – Sarkin Hausawan Amuwo Odofin

Spread the love

Daga DAUDA USMAN a Legas

An shawarci masu kuɗi da sauran attajiran ƙasar nan da su ci gaba da taimakon talakawa marasa shi da gajiyayyu da sauran makamantansu.

Mai martaba Sarkin Hausawan Ƙaramar Hukumar Amuwo Odofin dake cikin jihar Legas Alhaji Adamu Aliyu ɗan asalin jihar Jigawa mazaunin Legas, ya nemi hakan a lokacin gudanar da wa’azin watan Ramadan na karshen makon jiya.

Taron gudanar da wa’azin wanda ya gudana a harabar Qaramar Hukumar Amuwo Odofin dake cikin garin Legas wanda ya ƙunshi malamai da waɗansu daga cikin sarakunan Hausawa al’ummar Musulmi mazauna unguwarni daban-daban na yankin Qaramar Hukumar Amuwo Odofin gaba ɗaya.

Kaɗan daga cikin sarakunan Hausawan sun haɗa da Sarkin Hausawan Ƙaramar Hukumar Amuwo Odofin Alhaji Adamu Aliyu jagaba da Sarkin Hausawan Festac Alhaji Mustapha Musa Uban Tafiya da Sarkin Hausawan Kasuwar duniya a Legas Alhaji Musa Sale da sauran sarakunan Hausawa makamantan su.

Sarkin Hausawan ƙaramar hukumar Amuwo Odofin Alhaji Adamu Aliyu jagaba shi ne ya jagoranci sauran sarakunan Hausawa a wajen gabatar da wa’azin watan Ramadan na ƙarshen makon da ya gabata.

Manyan baƙi a wajen taron gudanar da wa’azin sun haɗa da Shugaban Ƙaramar Hukumar Amuwo Odofin Dakta Injiniya Valantine Oluwa da ɗan majalisar dokoki mai wakiltar ƙaramar hukumar Amuwo Odofin a zauren majalisar dokokin jihar Legas egas Hon kiki da sakatariyar Karamar hukumar Amuwo Odofin Misis Kemi Osho da shugaban jam’iyar APC na Legas ta Yamma da mataimakinsa Ayo Ogun Biyi da Seyi Buraimoh ambasadan neman zaman lafiya Amuwo Odofin da babban limamin masallacin Juma’a na Karamar Hukumar Amuwo Odofin da sauran makamantansu.

Bayan kammala wa’azin watan Ramadan na ƙarshen makon jiyan ne a jawaban Shugaban Ƙaramar hukumar Amuwo Odofin Dakta iInjiniya Valantine Oluwa da na ɗan majalisar dokokin jihar Legas da sarakunan Hausawa da sauran al’ummar Musulmi waɗanda suka samu yin tsokaci a wajen taron gudanar da wa’azin na wannan shekarar sun gabatar da muhimman jawaban waɗanda za su ƙara kawo zaman lafiya a tsakanin al’ummar Hausawa da sauran ƙabilu mazauna yankin gaba ɗaya.

Sannan Sarkin Hausawan ƙaramar hukumar Amuwo Odofin Alhaji Adamu Aliyu Jagaba ya cigaba da jawo hankulan masu kudi da sauran attajirai na ƙasar nan da su ci gaba da tallafa wa talakawa marasa shi da gajiyayyu a cikin wannan watan mai tsarki domin samun kyakkyawan sakamako a ranar gobe kiyama.

Haka zalika ya cigaba da jin jinawa al ummar hausawan da na karamar hukumar sa ta Amuwo Odofin akokaron su na cigaba da zaman lafiya sauran ƙabilu mazauna yankin gaba ɗaya.

By Editor