Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD
Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da kwamitin Majalisar Dattawa mai Kula da Ladaftarwa da ɗa’a daga ɗaukar matakin ladabtara a kan Natasha Akpoti-Uduaghan.
Mai shari’a Obiora Egwuatu, ya bayar da umarnin ne a ranar Talata bayan wata takardar da lauyoyin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (mai wakiltar Kogi ta tsakiya) suka gabatar.
An gayyaci Akpoti-Uduaghan da ta bayyana a gaban kwamitin ladabtarwa na majalisar dattijai bayan wata hatsaniya da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio a ranar 20 ga watan Fabrairu.
Idan za a iya tunawa, Sanata Akpoti-Uduaghan ta kawo cikas ga zaman majalisar ta hanyar ƙin amincewa da kujerar da aka ba ta, inda ta bijire wa umarnin Akpabio da kuma tada wani batu a kai a kai duk da cewa an yi watsi da su.
Daga bisani, majalisar dattijai ta miƙa Akpoti-Uduaghan ga kwamitin ɗa’a don duba matakin ladabtarwa.
A ranar 28 ga Fabrairu, a wata hira da aka yi da ita a gidan talabijin na Arise, Sanatan na Kogi ta yi zargin cewa rikicinta a majalisar ya fara ne bayan ta ƙi amincewa da buƙatar lalata da shugaban majalisar dattawan.
