Fadar Shugaban ƙasa ta yi raddi ga Atiku kan yunwa

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Fadar Shugaban ƙasa ta mayar da martani kan fargarwar da tsohon mataimakin shugaban ƙasar, Atiku Abubakar ya yi na cewa za a iya samu juyin-juya-hali sakamakon matsananciyar yunwa da matsin rayuwa da ake fama da shi a ƙasar.

Fadar ta yi watsi da kalaman a matsayin tsohon tunani da aka riga aka wuce.

Inda ta bayana kalaman tsohon mataimakin shugaban ƙasar a matsayin na siyasa ne tsagwaran sa.

Gwamnatin ta kuma jaddada cewa matakan da gwamantin ke ɗauka tuni suka fara ɗora ƙasar kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki a ƙasar.

A cewar fadar shugaban ƙasa, hauhawar farashin kaya a Nijeriya ya ragu a wata na biyar a jere a watan Agustan 2025, inda ya faɗi daga 21.88 a watan Yuli zuwa kashi 20.12, kamar yadda bayanai daga Hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) ta nuna.

Gwamnati ta kuma bayyana rarar cinikin da aka samu a tarihi, inda ba a fitar da mai ba a yanzu ya ba da gudunmawar kashi 48 na jimlar cinikin, kusan daidai da kashi 52 na ɗanyen mai.

Onanuga ya ci gaba da bayyana cewa, adadin kuɗaɗen ƙasashen waje ya ƙaru zuwa kusan dala biliyan 42, daga dala biliyan 32 lokacin da shugaba Tinubu ya hau mulki.

Ya kuma yi nuni da cewa, gwamnatin ta samu nasarar cire sama da dala biliyan 7 da aka gada daga cikin kuɗaɗen da ake bin su a ƙasashen waje da suka hada da dala miliyan 800 da ake bin kamfanonin jiragen sama na ƙasa da ƙasa.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “A ƙarƙashin Shugaba Tinubu, Nijeriya na samun kuɗaɗen shiga da ba a taba samu ba. Yanzu haka Jihohin ƙasar na iya biyan albashi da gratuti ba tare da ɓata lokaci ba, kuma har yanzu suna da rarar kuɗaɗe don gudanar da ayyukan jari da zamantakewa, nasarar da ba a taɓa gani ba a wannan sikelin.”

Fadar shugaban ƙasar ta kuma zargi Atiku da jam’iyyar adawa ta PDP da yin siyasa da ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta da kuma kasa ɗaukar alhakin abin da ta kira shekaru na taɓarɓarewar tattalin arziki a lokacin da suke mulki.

“Yawancin ƙalubalen da muke fuskanta a yau sun samo asali ne daga kurakuran tattalin arziki na shekarun PDP, lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban ƙasa. Shugaba Tinubu da tawagarsa suna aiki tukuru don gyara waɗannan kura-kurai tare da yin garambawul,” inji Onanuga.

A ƙarshe sanarwar ta sake jaddada aniyar shugaba Tinubu na samar da kyakkyawan sakamako ga ‘yan Nijeriya, inda ta jaddada cewa “bayan shekaru biyu da watanni biyar kacal a kan karagar mulki, muna alfahari da ci gaban da ake samu.

Alhaji Atiku Abubakar ya zargi gwamantin Bola Ahmed Tinubu da samar da manufofi da ke ƙara ta’azzara hauhawar farashi, da rashin aikin yi, da ƙarancin abinci a ƙasar.

By ukarofi