Tinubu zai iya karɓe ikon ’yan sandan jihohi idan gwamnoni sun yi amfani da su ba daidai ba – Barau

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya bayyana cewa tsarin da ake shirin samarwa na ’yan sandan jihohi ya ƙunshi tanade-tanaden kundin tsarin mulki da za su bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu damar shiga tsakani idan gwamnonin jihohi suka yi amfani da rundunar ta hanyar da ba ta dace ba.

Blueprint Manhaja ta ruwaito cewa Barau, wanda kuma shi ne shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Bita da Gyaran Kundin Tsarin Mulki, ya bayyana haka ne a ranar Asabar yayin wata tattaunawa a shirin Hannu Da Yawa na gidan rediyon Nijeriya da ke Kaduna.

Kalaman Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawar na zuwa ne makonni kaɗan bayan da Majalisar Dattawa ta amince da kudirin gyaran kundin tsarin mulki da ke neman kafa rundunar ’yan sandan jihohi, tare da tanade-tanade na musamman domin hana yiwuwar amfani da ita ba daidai ba daga gwamnatocin jihohi.

A ƙarƙashin wannan tsari, Nijeriya za ta gudanar da tsarin ’yan sanda biyu, inda Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya (NPF) da kuma rundunonin ’yan sandan jihohi za su yi aiki tare a lokaci guda. ƙudirin ya kuma fayyace yanayin da gwamnatin tarayya za ta iya shiga cikin harkokin rundunar ’yan sandan jihohi.

Barau ya bayyana yunƙurin Shugaba Bola Tinubu na kafa rundunar ’yan sandan jihohi a matsayin wani muhimmin mataki na magance matsalolin tsaron da ƙasar ke fama da su tsawon shekaru.

A cewarsa, ƙudirin ya samo asali ne bayan tattaunawa mai zurfi tsakanin Fadar Shugaban ƙasa, Majalisar Tarayya, Sufeto Janar na ’Yan Sanda, tsofaffin jami’an ’yan sanda, masana harkokin tsaro, gwamnoni, ƙungiyoyin farar hula da kuma al’umma baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa an kuma gudanar da sauraron ra’ayoyin jama’a a shiyyoyin siyasa shida na ƙasar nan da kuma Babban Birnin Tarayya, Abuja.

“Shugaba Tinubu ya yi nazari sosai kan lamarin, inda ya gano cewa duk da cewa mutane da yawa suna goyon bayan kafa ’yan sandan jihohi, akwai fargabar cewa za a iya amfani da su don muradun siyasa ko na ƙabilanci. Wannan ne ya sa aka gina kariya da matakan tsaro a cikin tsarin,” inji Barau.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawar ya bayyana cewa tsarin da ake shirin aiwatarwa ya ƙunshi kariya ta doka da kuma hanyoyin sa ido na hukumomi domin hana duk wani amfani da rundunar ba daidai ba.

“Idan aka yi amfani da ’yan sandan jihohi wajen tsoratarwa ko aikata abubuwan da za su yi barazana ga rayuka da dukiyoyi, Shugaban ƙasa na da ikon kundin tsarin mulki na shiga tsakani tare da umartar Rundunar ’Yan Sandan Tarayya ta karɓe ikon gudanar da ayyukan tsaro,” inji shi.

Barau ya bayyana cewa rundunar ’yan sandan jihohi za ta kasance ne domin ƙarfafa aikin Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya, ba wai maye gurbinta ba.

“Jami’an ’yan sandan jihohi, waɗanda za a ɗauko daga cikin al’ummomin yankunan da suke aiki, sun san mutane, sun san yankuna, har ma sun san masu aikata laifuka,” inji shi.

“Wannan zai taimaka matuƙa wajen magance matsalolin ’yan bindiga, garkuwa da mutane da sauran laifuka. Yankin Arewa zai amfana sosai daga wannan tsari. An tsara wannan shiri ne domin samar da zaman lafiya mai ɗorewa a yankunan da matsalar tsaro ta fi ƙamari.”

Ya kuma bayyana cewa yayin da Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya za ta ci gaba da kula da manyan batutuwan tsaro na ƙasa kamar ta’addanci da laifukan yanar gizo, rundunonin ’yan sandan jihohi za su fi mayar da hankali kan tsaron cikin gida da tabbatar da zaman lafiya da oda a cikin al’umma.

Barau ya kuma bayyana cewa za a naɗa kwamandojin rundunar ’yan sandan jihohi ne ta hanyar tsari mai tsauri, tare da tanadin kariyar doka domin hana tsoma bakin siyasa a ayyukansu.

Dangane da batun kuɗaɗen gudanarwa da ƙarfin aiki, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawar ya ce za a samar da tsare-tsaren kuɗi da gudanarwa da suka dace yayin da ake ci gaba da aikin gyaran kundin tsarin mulkin.

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa majalisun dokokin jihohi a faɗin ƙasar nan za su goyi bayan wannan shiri.

“Dole ne mu sake fasalin tsarin tsaronmu domin kare rayuka da dukiyoyi yadda ya kamata tare da hana duk wani amfani da iko ba daidai ba,” inji Barau.

“Wannan shiri ne da aka tsara cikin daidaito, tuntuba da kariya, tare da manufar kusantar da aikin ’yan sanda ga al’umma.”

By ukarofi

Leave a Reply