
Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI
Ministan yaɗa labarai da haɗin kan ƙasa, Mohammed Idris ya ce aikin tashar iskar gas na Ajaokuta-Kaduna-Kano, zai taimaka wajen inganta tattalin arziƙin Arewacin Najeriya.
Ministan ya faɗi haka ne ta ofishin mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Rabiu Ibrahim a yayin wani ziyaran gani da ido da ya kai wajen aikin a Jihar Kaduna tare da Ministocin kuɗi da tattali, Wale Edun da ƙaramin ministan albarkatun iskar gas, Ekperikpe Ekpo da kuma shugaban kamfanin NNPC, Mele Kyari.
Ya kuma ce, aikin zai sa a samu yawaitar amfani da iskar gas a gidaje da wajen sana’o’i da masarrafun abubuwa da ma kawo sauƙi har a harkokin sufuri.
Ministan ya ƙara da cewa, wannan aiki wani ɓangare ne na cika alƙawarin shugaba Tinubu na inganta harkar tattalin arziki a dukkan sassan Najeriya dan haka ya ke fatan a samu haɓakar tattalin arziƙin ƙasa da kuma inganta rayukan ƴan Najeriya musamman ƴan Arewa yayin kammala aikin.
