
Daga BELLO A. BABAJI
Shugaba Bola Tinubu ya aika da tawagar Nijeriya zuwa birnin Vatican domin halarta jana’izar Paparoma, wanda za a yi a yau Asabar, 26 ga watan Afrilu.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio shi zai jagoranci tawagar ta mutane biyar, kamar yadda Kakakin Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga ya bayyana a wata takarda, ranar Juma’a.
Sauran mambobin tawagar sun haɗa da Ƙaramar Ministar Harkokin Waje, Bianca Ojukwu; Archbishop Luscius Ugorji; Archishop Matthew Kukah da kuma Archbishop Ignatius Ayua Kaigama.
A ranar 22 ga watan Afrilun 2025 ne Paparoma, wanda shi ne shugaban Cocin Roman Catholic ya rasu, bayan shafe shekaru 88 a duniya, kwana ɗaya bayan bikin Easter a Fadar Vatican.
Tawagar za ta gabatar da saƙon Shugaban Nijeriya na jajenta wa al’ummar kiristoci bisa babban rashin jagoran nasu.
Tun a ranar Litinin ne Shugaba Tinubu ya shiga sahun ƴan ɗariƙar Katolika da sauran Kiristoci wajen jimamin mutuwar Pafaroma a matsayinsa na jigo acikin al’umma.
