Bom ya tashi a sakatariyar APC yayin da aka fara zaɓen ƙananan hukumomin Ribas

Spread the love

Daga BELLO A BABAJI

Wasu mutane da ake zargi sun sanya bom a sakatariyar jam’iyyar APC da ke Fatakwal a Ribas yayin da ake gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar a yau Asabar.

Wata ɗaukar bidiyo ta nuna yadda abin fashewar ya tarwatse a ƙofofin shiga sakatariyar.

Cikin wani gajeren saƙo da shugaban jam’iyyar na riƙon ƙwarya a jihar, Cif Tony Okocha ya aika wa manema labarai ya zargi magoya bayan Gwamnan jihar Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP da ɗanyen aikin.

Ana gudanar da zaɓen ne cikin lumana a sassa daban-daban na jihar duk da cewa rundunar ƴan sanda ta tsame hannunta acikin harkokin zaɓen sakamakon umarnin kotu.

Sannan, ana gudanar da zaɓen ne a gundumomi 319 da mazaɓu 6,366 a ƙananan hukumomi 23 na jihar.

Haka nan, sha takwas daga cikin halastattun jam’iyyu 19 a Nijeriya ke fafatawa a zaɓen.

By Babaji