Direbobin Dangote sun koka kan tsangwamar sabbin masu hannun jari

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Direbobin manyan motocin Kamfanin Dangote sun nuna damuwarsu kan abin da suka bayyana a matsayin fuskantar tsangwama daga wasu sabbin masu sayen hannun jarin kamfanin bayan ƙaddamar da sayar da hannun jarin Matatar Fetur ta Dangote (IPO).

A wani faifan bidiyo da Economic Confidential ta fassara daga Hausa zuwa Turanci, ɗaya daga cikin direbobin ya koka kan yadda wasu mutane ke tsayar da shi a hanya, suna iƙirarin cewa sun zama masu haɗin gwiwar mallakar motar saboda kawai sun sayi hannun jari a kamfanin.

A cewarsa, lamarin ya fara zama abin da ba za a iya jurewa ba. Ya ba da misali da cewa, “Jiya ina sauke kaya sai wani ya zo a kan babur. Bayan ya gaishe ni, sai ya tambaye ni, ‘Abokina, ya motarmu take?’ Na rikice, sai ya ce min yanzu shi ma yana da hannun jari a Dangote.”

Ya ƙara da cewa, wani mutum da ke cikin motar haya ma ya taɓa tsayar da shi, yana gargaɗin sa da kada ya sake tuƙa motar Dangote cikin sakaci, domin zai ba da shawarar a kore shi daga aiki, yana cewa shi ma sabon mai hannun jari ne.

Direban ya jaddada cewa duk da cewa babu abin da ya hana ’yan Nijeriya saka kuɗinsu a matatar, mallakar hannun jari ba yana nufin mutum ya mallaki kadarorin kamfanin ko kuma ya samu ikon ba da umarni ga ma’aikatansa ba.

Ya ce, “Bari in fayyace wannan: babu wanda ya kamata ya tsayar da ni ko ya gaya min na kula da yadda nake tuƙin motar Dangote. Hannun jarin da ka saya naka ne, kuma ba shi da alaƙa da aikina. Tun bayan da aka ƙaddamar da sayar da hannun jarin jiya, mutane uku sun riga sun zo gare ni suna gaya min na yi hankali wajen tuƙi.”

Direban ya roƙi jama’a da su daina tsangwamar masu tuƙin manyan motoci, yana mai cewa aikinsu kansa na da matuƙar wahala, don haka ba sa buƙatar ƙarin katsalandan daga sabbin masu hannun jari masu murna.

Kamfanin Matatar Man Fetur na Dangote ya ƙaddamar da sayar da hannun jarinsa ga jama’a a ranar Litinin, 14 ga Satumba, 2026, a wani mataki da wasu manazarta suka bayyana a matsayin mafi girman sayar da hannun jari ga jama’a a tarihin Afirka.

Kamfanin na bayar da hannun jari na yau da kullum biliyan 4.1, inda aka sanya farashin kowane hannun jari a Naira 525, da nufin tara kusan Naira tiriliyan 2.15, kwatankwacin dala biliyan 1.6. Mafi ƙarancin adadin hannun jarin da mutum zai iya saya shi ne guda 10.

An buɗe sayar da hannun jarin ne a Kasuwar Hada-Hadar Hannayen Jari ta Nijeriya (NGɗ), kuma za a rufe shi a ranar 13 ga Oktoba, yayin da ake sa ran za a fara sayar da hannun jarin a kasuwar hannayen jari a watan Nuwamba na 2026.

Wanda ya kafa rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya ce an tsara sayar da hannun jarin ne domin bai wa miliyoyin ’yan Nijeriya da ’yan Afirka damar mallakar kaso a babbar matatar mai a nahiyar, tare da samar wa kamfanin kuɗin faɗaɗa ayyukansa.

By ukarofi

Leave a Reply