Filato: Hedikwatar Tsaro ta gayyaci shugaban CAN kan zargin sojoji da kisa

Spread the love

Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Hedikwatar Tsaro ta sojoji ta bayyana aniyar ta na ganawa da Rev Timothy Daluk, Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya a Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Daluk ya zargi sojojin Nijeriya da sa ido kan kashe-kashen Kiristoci da lalata dukiyoyi a jihar.

A wani faifan bidiyo da ya fito, Daluk ya yi zargin cewa sojojin Nijeriya na da hannu wajen kashe Kiristoci da varnata dukiya a jihar.

Ya yi ikirarin cewa sojoji na da hannu wajen korar Kiristoci tare da barin wasu gungun ’yan bindiga sun kona gidajensu a karamar hukumar Mangu.

A halin da ake ciki, gwamnatin jihar Filato ta yi kira ga hukumomin sojin kasar da su binciki zargin nuna son rai da ake yi akan sojoji a karamar hukumar Mangu, inda aka kashe mutane 30 a ranar Laraba.

Kwamishinan yada labarai na jihar Filato, Musa Ashoms, wanda ya bukaci hakan a wata hira da aka yi da shi ranar Laraba, ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su rungumi zaman lafiya.

By Editor