
Daga BELLO A. BABAJI
Gwamnatin Tarayya na shirin ƙaddamar da biyan ma’aikata kuɗaɗen bashi da N35,000 ga kowannen su har na tsawon wata biyar.
Daraktan yaɗa labarai na Ofishin akanta-janar na ƙasa OAGF, Bawa Mokwa ya bayyana hakan a wata takarda.
Ya ce, da farko dai Gwmantin Tarayya ta biya ma’aikata albashin ne da kaɗan-kaɗan na wa’adin watanni biyar, inda a yanzu ma za a riƙa biyan su N35,000 a kowane wata don biyan su bashin da suke bin ta.
Ya kuma ce, wanda za a fara biya shi ne na watan Afrilun shekarar 2025.
Haka kuma ya ce, gwamnatin ta na iya ƙoƙarinta wajen ganin ta aiwatar da tsare-tsaren kyautata hanyoyin biyan ma’aikata don walwalarsu da kuma ƙara masu ƙwarin-gwiwa wajen sauke nauye-nauyen da aka ɗora masu.
