
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Babban taron jam’iyyar PDP ka iya fuskantar ƙalubale duba da cewa babu wakilci na musamman daga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC).
An gano haka ne a lokacin da Gwamnan Jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya bayyana haka a wani jawabin faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen yaɗa labarai.
Ya kuma ce, INEC ba ta turo wakilanta ba domin sanya ido akan taron jam’iyyar, wanda ake gudanarwa a filin wasa na Lekan da ke Birnin Ibadan a Jihar Oyo.
Haka kuma gwamnan ya nesanta kansa da batun nan na sallamar Ministan Abuja, Nyesom Wike da wasu jiga-jigan jam’iyyar daga cikinta.
Haka ma takwaransa kuma Gwamnan Jihar Filato, Caleb Manasseh Mutfwang a wata sanarwa daga Kakakinsa, Gyang Bere, wanda ya ce ƙungiyar gwamnoni ba ta taɓa tattauna batun korar mambobin nata ba, sannan a kwamitin zartarwar jam’iyyar gabanin gabatar da shi a taron.
Ya bayyana cewa, babu hikima cikin korar wasu jiga-jigan jam’iyyar a yanzu musamman ganin yadda take buƙatar tattaro kawunan ƴaƴanta wajen dawo da martabarta.
