Jam’iyyar APC a Zamfara ta yaba da naɗin Yari da Matawalle jami’an kamfen ɗin Tinubu

Spread the love

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau

Jam’iyyar All Progressives Congress, APC, reshen Jihar Zamfara ta bayyana naɗin Sanata Abdulaziz Yari Abubakar da ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle a matsayin shugabannin kwamitin yaƙin neman zaɓen Shugaban ƙasa na 2027.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Ibrahim Muhammad ya sanya wa hannu yau Asabar, shugaban jam’iyyar na jihar Hon. Kabiru Moyi Birnin Magaji, ya bayyana cigaban a matsayin wata alama mai kyau ga jam’iyyar kafin babban zaɓen ƙasa.

Hon. Moyi ya ce mambobin jam’iyyar APC a Zamfara suna da cikakken ƙwarin gwiwa cewa shigar shugabannin Zamfara biyu ba wai kawai zai tabbatar da nasara ga Shugaba Tinubu ba, har ma da dukkan ‘yan takarar APC a jihar da ƙasa baki ɗaya.

Ya lura cewa naɗin ya nuna irin gogewar siyasa da shugabanci da dukkan mutanen biyu suka kawo a kamfen ɗin shekarar 2023.

Ya ƙara da cewa, jam’iyyar APC tana da matsayi don ci gaba da samun nasara a kowane fanni.

Ya yaba wa shugaba Tinubu da shugabannin APC na ƙasa bisa hangen nesa da suka yi wajen naɗin haka kuma, ya taya waɗanda aka naɗa murna bisa abin da ya kira girmamawar da ta cancanta.

Hon. Moyi ya tabbatar wa majalisar yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa cewa za su cigaba da goyon baya da haɗin gwiwa na tsarin jam’iyyar APC a jihar ta Zamfara don cimma sakamakon da ake so a shekarar 2027.

By ukarofi

Leave a Reply