Layin dogo na Abuja zuwa Kaduna zai koma aiki mako mai zuwa, inji NRC

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Hukumar kula da Tashoshin Jiragen ƙasa (NRC) ta ce layin dogo na Abuja zuwa Kaduna zai koma aiki nan da mako mai zuwa.

Hakan ya biyo bayan kammala gyara a sashen da ya lalace da kuma nazari a kai daga ƙwararru game da inganci tsaronsa, kamar yadda jami’in hulɗa da jama’a, Callistus Unyimadu ya bayyana.

Ya ce, za a sanar da ƙarin bayani akan al’amarin da kuma ranar da za koma aikin nan ba da jimawa ba.

Jami’in ya bayyana cewa, tun da aka ɗauki matakin dakatarwar na wucin-gadi bayan gocewar wani jirgi da ya nufi Kaduna daga Abuja, hukumar ta ke aiki tuƙuru wajen tabbatar da warware matsalar bisa inganci da nagarta kamar yadda ake yi a tsarin layukan a ko’ina a duniya.

NRC ta kuma ce, a ƙoƙarinsa na kula da walwalar fasinjoji, ta mayar wa mutane 512 kuɗaɗensu daga cikin fasinjoji 583 da ke cikin jirgin a lokacin da abin ya faru.

Ta ƙara da cewa, ana ƙoƙarin ganin su ma sauran fasinjojin da suka rage a mayar musu da kuɗaɗen nasu.

By Babaji