Mahukuntan sojin Nijar sun haramta fitar da shinkafa, hatsi da sauran kayan abinci zuwa wasu ƙasashe sai dai ƙasashen membobin Kungiyar Alliance of Sahel States (ASS).
Kungiyar ASS ƙungiya ce da aka kafa tsakanin Mali, Nijar da Burkina Faso a matsayin yarjejeniyar tsaro bayan rikicin Nijar na shekarar 2023, inda ƙungiyar siyasa ta yammacin Afirka ECOWAS ta yi barazanar tsoma baki ta hanyar soji don dawo da mulkin farar hula bayan juyin mulki a Nijar a farkon shekarar.
Gwamnatin ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a daren Laraba cewa shugaban ƙasa Abdourahamane Tiani ya ɗauki wannan mataki domin kare kayayyakin abinci na cikin gida da kuma fitar da kayayyakin amfanin yau da kullum a farashi mai sauki.
Waɗannan haramcin ba su shafi fitarwa zuwa ƙasashen Mali da Burkina Faso ba,” in ji sanarwar, ƙasashen dake da haɗin kai da Nijar kuma a halin yanzu suna ƙarƙashin jagorancin sojojin da suka karɓi mulki ta hanyar juyin mulki.
Hukuncin da zai hau kan masu laifin karya wannan doka ya haɗa da karɓar kayayyakin da aka kama da kuma hukunci na shari’a.
Nijar muhimmiyar mai samar da hatsi ce a yankin, musamman ga wasu jihohin ƙasar Najeriya.
Ko da yake an dage takunkuman da ƙungiyar ECOWAS ta ƙaƙaba wa Nijar bayan juyin mulkin watan Yulin 2023 a watan Fabrairu, hakan bai hana tasgaro ga kayayyakin abinci zuwa kasuwannin Nijar ba, inda hauhawar farashi ke ci gaba da shafar kayayyaki kamar shinkafa.
Rufe iyakar dake tsakanin Nijar da Benin shima ya taka muhimmiyar rawa wajen haifar da wannan matsalar.
Ministan noma ya yi alkawarin sayen wani kaso na amfanin gonar manoma don cike manyan ajiyoyin kayayyakin gaggawa na ƙasar.
Ma’aikatar ta ce tana fatan samun “kyakkyawan amfanin gona” duk da ambaliyar ruwa ta yi barna a sassan ƙasar ta yammacin Afirka.
