RMAFC ta ƙaddamar da shirin tantancewa don adalci a rabon kuɗin shiga

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Hukumar Tattara Kuɗaɗen Shiga, Rabon Albarkatu da Harkokin Kuɗi (RMAFC) ta fara wani muhimmin shiri na tantance bayanai a dukkan jihohin Nijeriya da Babban Birnin Tarayya Abuja, domin inganta tsarin rabon kuɗaɗen shiga na ƙasa da tabbatar da adalci wajen rabon albarkatu.

Shirin, wanda ake gudanarwa a faɗin ƙasar baki ɗaya, na da nufin sake duba muhimman ƙa’idoji da ƙididdiga da ake amfani da su wajen raba kuɗaɗen shiga tsakanin jihohi da ƙananan hukumomi, tare da daidaita su da halin tattalin arziki da zamantakewa na yanzu.

Shugaban hukumar, Mohammed Bello Shehu, ya bayyana wannan mataki a matsayin wani ginshiƙi mai muhimmanci wajen ƙarfafa tsarin rabon iko na kuɗi da kuma inganta tsare-tsaren ci gaban ƙasa. Ya jaddada cewa sahihan bayanai ne tushen adalci, gaskiya da kuma daidaito wajen rabon dukiyar ƙasa.

A cewarsa, wannan tantancewa za ta samar da sabbin bayanai masu inganci da za su taimaka wajen kammala duba tsarin raba kuɗaɗen shiga na ƙasa, wanda ya ce ya kai mataki na gaba.

“Mun ƙuduri aniyar tabbatar da cewa tsarin rabon kuɗaɗen Nijeriya ya dace da gaskiyar halin da ake ciki a ƙasa. Sahihan bayanai su ne ginshiƙin adalci da haɗin kan ƙasa,” inji shi.

Shirin zai haɗa da tattarawa, tantancewa da kuma daidaita bayanai kan al’amuran zamantakewa da tattalin arziki da ake amfani da su wajen ƙididdige rabon kuɗaɗe. Daga cikin abubuwan da ake dubawa akwai yawan jama’a, ilimi, kiwon lafiya, ƙarfin tattara kuɗaɗen shiga na cikin gida, ci gaban ababen more rayuwa da kuma faɗin ƙasa.

Dekta Shehu ya bayyana cewa sauye-sauyen da suka faru a Nijeriya a ‘yan shekarun nan—ciki har da ƙaruwa a yawan jama’a, bunƙasar birane da kuma bambance-bambancen ci gaba—sun sa ya zama wajibi a riƙa sabunta bayanai lokaci-lokaci domin samar da tsarin kuɗi mai adalci.

A wani ɓangare na shirin, tawagogin RMAFC za su yi aiki tare da ma’aikatu, sassa da hukumomin gwamnati, da gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi, da kuma sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin farar hula da shugabannin al’umma domin tabbatar da sahihancin bayanai da cikakken haɗin kai.

Haka kuma, za a gudanar da tarukan masu ruwa da tsaki a sassa daban-daban na ƙasar domin ƙara bayyana gaskiya, gina amincewar jama’a da kuma karɓar shawarwari daga kowane ɓangare.

Hukumar ta jaddada cewa wannan aiki na daga cikin wajibcin doka, tare da zama wani muhimmin tsari na ƙasa da ke nufin ƙarfafa sahihancin hukumomi da kuma tsara manufofi bisa hujjoji.

Ana sa ran sakamakon wannan shiri zai yi tasiri mai faɗi ga tsarin kula da kuɗaɗe, tsare-tsaren ci gaban ƙasa da kuma daidaita cigaban yankuna daban-daban na Nijeriya.

By ukarofi