Shugaban NYCN a Giwa ya bu ƙaci gwamnatin Kaduna ta ƙara zuba jari a cigaban yankin

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Shugaban  ƙungiyar Matasan Nijeriya (NYCN), reshen  ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna, Kwamared Nuhu Haruna Sani, wanda aka fi sani da Alkurkawee, ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar Eid-el-Fitr, inda ya yi musu fatan alheri da zaman lafiya.

A cikin sa ƙonsa na Sallah, Kwamared Alkurkawee ya bayyana muhimmancin wannan lokaci na  ƙaramar Sallah a matsayin dama ta  ƙara dan ƙon zumunci, yafiya da kuma taimakon juna a tsakanin al’umma, musamman bayan kammala ibadar azumin watan Ramadan.

Ya kuma bu ƙaci al’ummar Giwa da su ci gaba da zama cikin ha ɗin kai da juna tare da kiyaye dokoki da  ƙa’idoji domin tabbatar da zaman lafiya mai  ɗorewa a yankin.

Hakazalika, shugaban na NYCN ya yi kira ga gwamnatin jihar Kaduna  ƙar ƙashin jagorancin Gwamna Uba Sani da ta  ƙara mayar da hankali kan ayyukan raya  ƙasa a  ƙaramar Hukumar Giwa, musamman a  ɓangarorin ababen more rayuwa, ilimi, lafiya da kuma samar da ayyukan yi ga matasa.

Ya jaddada cewa  ƙaramar Hukumar Giwa na da matu ƙar bu ƙatar  ƙarin kulawa daga gwamnati domin inganta rayuwar al’umma da kuma bun ƙasa tattalin arzikin yankin.

A  ƙarshe, Kwamared Nuhu Haruna Sani Alkurkawee ya yi addu’ar Allah ya kar ɓi ibadun Musulmi, ya kawo zaman lafiya a Nijeriya, tare da bai wa shugabanni hikima da basirar tafiyar da al’amuran al’umma yadda ya kamata.

By ukarofi