Daga CMG HAUSA
Yau Alhamis ne shugaba Xi Jinping na ƙasar Sin, da takwaransa na ƙasar Congo (Kinshasa) Félix-Antoine Tshisekedi Tshilombo, suka aikewa juna sakon murnar cika shekaru 50 da ɗora hulɗar da ke tsakanin ƙasashen 2 kan hanyar da ta dace.
A cikin saƙonsa, Xi ya nuna cewa, a rabin ƙarnin da ya gabata, ƙasashen 2 sun raya hulɗa a tsakaninsu yadda ya kamata, sun kuma rika zurfafa dankon zumunci a tsakaninsu.
A shekarun baya, ƙasashen biyu sun kafa hulɗar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, kuma haɗin gwiwarsu ya haifar da sakamako mai yawa, kuma hakan ya amfani al’ummomin ƙasashen biyu.
Xi ya kara da cewa, yana dora muhimmanci kan raya dangantaka a tsakanin ƙasar Sin da ƙasar Congo (Kinshasa), yana kuma son yin ƙoƙari tare da shugaba Félix-Antoine Tshisekedi Tshilombo, wajen yin amfani da damar cika shekaru 50 da ɗora hulɗar ƙasashen biyu a kan hanyar da ta dace, domin zurfafa amincewar juna ta fuskar siyasa, da inganta haɗin gwiwarsu a fannin aiwatar da shawarar “ziri ɗaya da hanya ɗaya”, da kuma bude sabon babi na bunƙasar hulɗar da ke tsakanin ƙasashen biyu.
A nasa ɓangaren, Félix-Antoine Tshisekedi Tshilombo ya ce, a cikin shekaru 50 da suka wuce, ƙasarsa da Sin sun bunƙasa hulɗa a tsakaninsu yadda ya kamata ba tare da kasala ba.
Yana kuma fatan kara zurfafa dankon zumunci a tsakanin ƙasashen biyu, da ƙara azama kan samun sabbin sakamako wajen bunkasar hulɗar abokantaka a tsakanin ƙasashen biyu bisa manyan tsare-tsare, a ƙoƙarin kawo wa jama’ar ƙasashen biyu alheri.
Mai fassara: Tasallah Yuan