Tilasta zubar da ciki a Arewa maso Gabas: An tuhumi ƙungiyar Medecins Sans Frontieres

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Hukumar Kare Haƙƙin bil’adama ta ƙasa (NHRC) a ranar Larabar da ta gabata ta shawarci Gwamnatin jihar Borno da ta tantance ayyuka da shirye-shiryen ƙungiyar Medecins Sans Frontieres a jihar.

An rawaito cewa hukumar ta bayar da wannan shawarar ne a cikin wani rahoto da ta gabatar wa jihar, wanda ya wanke sojojin Nijeriya daga hannu a rahoton tilasta mata 10,000 zubar ciki a yankin Arewa maso Gabas.

A ranar 7 ga Disamba, 2022, kamfanin dillancin labarai na Reuters ya wallafa wani rahoto da ke cewa tun daga shekarar 2013, sojojin Nijeriya sun gudanar da wani shiri na sirri, inda suka tilasta mata zubar da ciki ba bisa ƙa’ida ba a yankin Arewa maso Gabas, tare da kawo ƙarshen ciki aƙalla 10,000 a tsakanin mata da ‘yan mata, waɗanda yawancinsu aka yi garkuwa da su aka musu fyaɗe.

Bayan buga wa kamfanin dillancin labarai na Reuters, NHRC ta kafa wani kwamiti mai zaman kansa, kwamitin bincike mai zaman kansa na musamman kan take haƙƙin bil Adama a ayyukan yaƙi da tada ƙayar baya a arewa maso gabas, wanda wani alƙalin kotun koli mai ritaya, Justice Abdul Aboki ya jagoranta.

Da take jawabi gabanin gabatar da rahoton, babbar mai ba da shawara ga sakatariyar hukumar ta NHRC, Hillary Ogbonna, ta ce babu wata shaida da ke alƙanta sojojin Nijeriya dƙ shirin tilasta mata 10,000 zubar da ciki ba bisa ƙa’ida ba a yankin Arewa maso Gabas.

Ogbonna ya bayyana cewa masu fallasa sun shaida cewa wata ƙungiya mai zaman kanta, Medecins Sans Frontieres, na da hannu a shirin zubar da ciki a yankin Arewa maso Gabas.

Ya ce, MSF ta ƙi bayyana a gaban kwamitin.

Sai dai Ogbonna ya fayyace cewa sauran ƙungiyoyi masu zaman kansu ba sa aikin zubar da ciki a yankin Arewa maso Gabas.

Ya kuma bayyana cewa rashin bayyanar da kamfanin dillancin labarai na Reuters, kwamitin Red Cross na ƙasa da ƙasa (ICRC) ya sanya ayar tambaya game da sadaukar da kai ga ɗabi’u da ƙa’idojin da ta saba tsarawa.

By ukarofi