Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya taya tawagar Nijeriya murnar bajintar da ta nuna a Gasar Commonwealth da aka gudanar a birnin Glasgow na ƙasar Scotland, bayan da ta lashe jimillar lambobin yabo 24.
Tawagar Nijeriya ta samu lambobin zinariya 10, azurfa bakwai da tagulla bakwai, lamarin da ya sanya ƙasar cikin waɗanda suka yi fice a gasar.
A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar, shugaban ya yaba wa ’yan wasan saboda jajircewa, ƙwazo da kuma nuna ruhin kishin ƙasa da ya ɗaukaka martabar Nijeriya a idon duniya, inji sanarwar.
Shugaba Tinubu ya ce nasarorin da tawagar ta samu sun nuna irin ƙoƙari, horo da sadaukarwar da ’yan wasan suka yi domin kai wa wannan matsayi, inji sanarwar.
Ya kuma yaba wa Kwamitin Olympics na Nijeriya da Hukumar Kula da Wasanni ta ƙasa bisa ci gaba da tallafa wa ’yan wasa da bunƙasa harkokin wasanni a ƙasar, inji sanarwar.
Shugaban ya bayyana fatan cewa ƙwarewar da ’yan wasan suka samu a gasar za ta taimaka musu wajen samun manyan nasarori a sauran gasa na duniya da za a gudanar nan gaba.
Haka kuma ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da saka hannun jari a fannin wasanni, inganta cibiyoyin horas da ’yan wasa da kuma samar da ƙarin damammaki ga matasan Nijeriya domin su haskaka a matakan nahiya da na duniya, inji sanarwar.
