Tinubu ya umarci ministoci su gabatar da rahoton ayyukansu ga ’yan Nijeriya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci dukkan ministocin gwamnatinsa da su bayar da cikakken rahoton yadda suke tafiyar da ayyukansu ga ’yan Nijeriya a nan take.

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na ƙasa Mohammed Idris ne ya sanar da umarnin shugaban ƙasar a wani taron manema labarai a Abuja ranar Talata.

Ministan ya ce, rahoton ministocin zai bai wa ‘yan Nijeriya damar sanin abubuwan da gwamnati ta yi da kuma yin tambayoyi kan su.

Akwai ministoci 48 a majalisar ministocin Tinubu. Daga cikin su akwai Nyesom Wike, ministan babban birnin tarayya; Adebayo Adelabu, ministan wutar lantarki; David Umahi, ministan ayyuka, Olubunmi Tunji-Ojo, ministan cikin gida, da dai sauransu.