Yadda tsadar haya ke tilasta dubban ma’aikatan Legas koma wa yankin Ogun

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Matsalar tsadar rayuwa da ke ƙara tsananta a Nijeriya ta fara sauya tsarin zaman jama’a a Jihar Legas, inda dubban mazauna birnin ke ci gaba da barin tsakiyar gari zuwa unguwanni marasa tsada da kuma garuruwan da ke kewaye da Legas domin samun gidajen haya masu sauƙin biya.

Rahotanni sun nuna cewa hauhawar farashin kayayyaki, tashin kuɗin sufuri da kuma ƙarin kuɗin abinci sun jefa iyalai da dama cikin mawuyacin hali, lamarin da ya sa samun gida mai kyau a Legas ya zama tamkar abin alatu ga masu ƙarami da matsakaicin ƙarfi.

Masana harkokin gidaje sun bayyana cewa kasuwar gidaje da filaye ta kai wani matsayi mai wahala a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda kuɗin haya ke ƙaruwa cikin sauri fiye da yadda albashin ma’aikata ke ƙaruwa.

A sassa daban-daban na Legas kamar Ajah, Agege, Surulere da Shomolu, masu gidaje na ci gaba da ƙara kuɗin haya duk da ƙalubalen tattalin arzikin da jama’a ke fuskanta. A yanzu, kuɗin hayar ɗakin kwana biyu na iya kaiwa tsakanin Naira miliyan 1.5 zuwa miliyan 4 a shekara, yayin da a yankuna masu tsada kamar Lekki Phase 1, Victoria Island da Ikoyi haya ke kaiwa tsakanin Naira miliyan 5 zuwa miliyan 15 a shekara.

Sakamakon wannan matsin lamba, dubban iyalai, ma’aikata da matasa masu sana’o’i sun fara komawa yankunan da ke wajen Legas ko kuma makwabciyar Jihar Ogun, inda kuɗin haya ya fi sauƙi, duk da cewa hakan na nufin ƙarin wahalar zirga-zirga zuwa wuraren aiki.

Yanzu haka mutane da dama na zaune a garuruwa kamar Mowe, Ibafo, Sango-Ota, Agbado, Sagamu, Ota da Abeokuta, amma suna ci gaba da aiki a Legas, abin da ya haifar da yawan zirga-zirgar yau da kullum tsakanin jihohin Legas da Ogun.

Wani ma’aikaci mai suna Taiwo Akorede ya bayyana cewa ya tilasta komawa Mowe tare da iyalinsa saboda tsadar haya a Legas. Ya ce duk da cewa ya samu sauƙin haya, wahalar zuwa aiki ta ƙaru sosai.

“Haya ce ta sa na bar Legas. Amma yanzu kuɗin mota ya ninka, kuma wani lokaci sai na kwana a wurin aiki domin kada na makara,” inji shi.

Hakazalika, wani malamin makarantar sakandare mai suna Taiwo Adesanya ya ce ya bar Legas bayan mai gidansa ya ƙara masa haya daga Naira 900,000 zuwa Naira miliyan 2.2.

Ya ce, “A Mowe haya ba ta kai rabin abin da ake biya a Legas ba. Aƙalla yara na suna samun abinci kuma muna iya ci gaba da rayuwa.”

Masu dillancin gidaje sun tabbatar da cewa buƙatar gidaje a yankunan kan iyakar Ogun da Legas ta ƙaru matuƙa cikin shekaru biyu da suka gabata. Wani dillali mai suna Biodun Olatunji daga Sango-Ota ya ce yanzu ma’aikatan bankuna, jami’an gwamnati, ‘yan kasuwa da sauran ƙwararru na ta kwararowa yankin saboda tsadar rayuwa a Legas.

A cewarsa, hayar ɗakin kwana biyu a yankin na tsakanin Naira 400,000 zuwa Naira 700,000 a shekara, abin da ya sa iyalai da dama ke ganin ya fi dacewa da halin da suke ciki.

Sai dai masana harkokin gidaje sun yi gargadin cewa wannan yanayi alama ce ta manyan matsalolin da ke addabar ɓangaren gidaje a Legas. Sun bayyana cewa jihar na fama da giɓin gidaje sama da miliyan uku, kuma yawan jama’a na ci gaba da ƙara wannan matsala.

Malamar Tsare-tsaren Birane ta Jami’ar Legas, Dakta Funke Adeyemi, ta ce akwai buƙatar gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa. Ta ce, gwamnati ita kaɗai ba za ta iya magance matsalar ba, don haka dole ne a samar da ƙarfafawa ga masu zuba jari a harkar gidaje, da tsara dokokin kula da haya, tare da inganta ababen more rayuwa a garuruwan da ke kewaye da Legas.

A halin yanzu, yawan mutanen da ke shiga da fita Legas daga Ogun ya jefa manyan hanyoyi kamar Legas-Ibadan Eɗpressway, Legas-Sagamu Eɗpressway da Abeokuta Eɗpressway cikin cunkoson ababen hawa mai tsanani.

Dubban matafiya na shafe sa’o’i biyu zuwa huɗu a hanya kullum kafin su isa wuraren aikinsu. Wasu ma na tashi tun ƙarfe 4:30 na asuba domin kauce wa cunkoso. Wata ma’aikaciyar kula da kwastomomi mai suna Ngozi Eze ta ce ta kan isa wurin aiki a gajiye saboda tsawon lokacin da take ɗauka tana zirga-zirga daga wajen Legas.

Masana tattalin arziki sun yi gargaɗin cewa ci gaba da ƙauracewar jama’a daga tsakiyar Legas zuwa garuruwan kewaye na iya yin tasiri ga yawan aiki, tsare-tsaren birane da kuma ƙarfin ababen more rayuwa a jihohin Legas da Ogun.

Duk da cewa gwamnatin Ogun ta bayyana yawaitar masu ƙaura zuwa jihar a matsayin wata dama ta bunƙasa tattalin arziki, mazauna yankunan sun ce har yanzu suna fama da matsalolin hanyoyi, cunkoson ababen hawa da kuma ƙarin tsadar rayuwa.

By ukarofi