A kwanakin baya ne Hukumar Zaɓe Mai Zamanta Kanta ta Nijeriya (INEC) ta gargaɗi jam’iyyun siyasa da magoya bayansu da su guji fara yaƙin neman zaɓe gabanin zaɓukan 2027, inda ta bayyana hakan a matsayin karya dokar zaɓe.
Gargaɗin na INEC ya zo ne a daidai lokacin da ake samun yawaitar tarukan siyasa a faɗin ƙasar, da sanya allunan hotunan ‘yan takara a allunan talla.
Duk da cewa fara yaƙin neman zaɓe da ‘yan siyasar Nijeriya ke yi ba sabon abu ba ne, amma lamarin ya ƙara ta’azzara a siyasar da ke faruwa a halin yanzu da ayyukan gamayyar jam’iyyar ADC da ke neman kauda shugaban ƙasa mai ci Bola Ahmed Tinubu daga kan karagar mulki a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Fara yaƙin neman zaɓe kafin lokaci, hukumar ta INEC ta ce irin waɗannan ayyukan ba wai kawai bai dace ba har ma sun saɓa wa dokar zaɓe ta 2022.
Sakataren yaɗa labaran shugaban hukumar ta INEC, Rotimi Oyekanmi, ya ce har yanzu hukumar ba ta fitar da jadawalin zaɓen 2027 ba.
Oyekanmi ya bayyana cewa duk da ’yan Nijeriya na da ’yancin shiga tattaunawa ta siyasa da bayyana ra’ayoyinsu kan zaɓuka masu zuwa, duk wata buɗaɗɗiyar kamfen ko jefa ƙuri’a a zaɓen 2027 ba wai kawai bai dace ba har ma da karya dokar zaɓe.
Kazalika ba a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyu ba, kuma babu wata jam’iyyar siyasa da ta fitar da sunayen ’yan takara a babban zaɓen mai zuwa ba, yin hakan ya saɓa wa sashi na 94,(1) na dokar zaɓe ta 2022.
Oyekanmi ya ce, “An jawo hankalin dukkan jam’iyyun siyasa a Nijeriya kan wannan lamarin a taron tuntuɓa da muka yi na watanni uku na ƙarshe, kuma hukumar na sa ran samun cikakken bin doka.”
Gargaɗin na zuwa ne yayin da manyan ‘yan siyasa ciki har da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, gwamnonin jam’iyyar APC da kuma magoya bayansu da magoya bayansu ke tsara dabarun tunkarar zaɓen 2027.
To amma a cikin burinsu na ko dai su kwace mulki, a ɓangaren ‘yan adawa, ko kuma su ci gaba da riƙe shi, a ɓangaren jam’iyya mai mulki, ‘yan siyasar Nijeriya da jam’iyyunsu sun wuce gona da iri wajen saɓa wa dokokin ƙasa ta hanyar fara yaƙin neman zaɓe da sunan sake fasalin ƙasa ko kuma su koma kan zaɓe mai zuwa. Wannan aiki na rashin bin doka da oda ba wai kawai cutarwa ce ga kyakkyawan shugabanci ba; ya saɓa wa juyin mulkin dimokuraɗiyyar ƙasa.
Babban manufar gwamnati, kamar yadda yake cikin sashe na 14 (2) (b) na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya na 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima) shi ne tsaro da jin daɗin al’umma. Wannan yana nuna cewa ayyuka da manufofin gwamnati yakamata su fi mayar da hankali kan tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan ƙasa. Bugu da ƙari, kundin tsarin mulkin ya jaddada cewa mulki na al’umma ne kuma ya kamata su shiga cikin gwamnatoci.
Ba tare da shakka ba, wannan gagarumin tanadi na kundin tsarin mulki ya sha kaye a farkon fara yaƙin neman zaɓe, musamman nau’i da yanayin da a halin yanzu haɗin gwiwar ADC ke aiwatarwa wanda ke haifar da yaɗa kalaman ƙiyayya da farfagandar da ke tunzura ‘yan ƙasa a kan gwamnatinsu.
A baya-bayan nan ne dai gwamnatin tarayya ta samu dalilin ƙaryata rahotannin da kafafen yaɗa labarai ke yaɗawa na cewa shugaba Tinubu ya shagala da ɓullowar gamayyar jam’iyyar adawa ta ADC. Da yake ƙaryata rahoton, Ministan yaɗa labarai da wayar da kai, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Tinubu ta jajirce wajen gudanar da ayyukanta na samar da sauye-sauye masu ma’ana da haɓakar tattalin arziki ga ‘yan Nijeriya ne ba wai zaɓen 2027 ba.
A martanin da ya fito fili game da yunƙurin da ake zargin gwamnati na yi na yin kaca-kaca da ‘yan adawa, Idris ya tabbatar da ‘yancin yin amfani da ‘yancin faɗin albarkacin baki da kundin tsarin mulkin Nijeriya ya ba su, amma ya ƙara da cewa Tinubu ba zai bar baya da ƙura ta hanyar siyasa ko karkatar da hankulan jama’a ba.
Kamar yadda kamfanin Blueprint ya yaba wa INEC bisa kan lokaci da kuma gargaɗin da ta yi game da yaƙin neman zaɓe da jam’iyyun siyasa da masu neman takararsu ke yi tun da wuri, yana da kyau a buƙaci alƙalan zaɓen da su yi amfani da murya. Dole ne INEC ta wuce gargaɗi kawai don aiwatar da tanade-tanaden dokar zaɓe a kan waɗanda suka karya ta domin ta zama hanyar daaile ƙara karya dokar.
A nata ɓangaren, jam’iyyun siyasa da masu son tsayawa takara su yi ƙoƙarin kaucewa saɓa wa doka. Kamata ya yi su zama masu haɗin kai a cikin aikin gina ƙasa maimakon zama kwarkwata a turbar ci gaba.
