Ina neman addu’ar al’umma kan halin da nake ciki – Ɗan Sandan Ma’aiki

Spread the love

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano

Wani ɗan sandan Nijeriya da ke Kano, ASP Tijjani Muhammad Mila Ƙofar Wambai, wanda aka fi sani da Ɗan Sandan Ma’aiki, wanda kuma ya shahara wajen yin waƙoƙin yabon Fiyayen Halita Annabi Muhammad (SAW) sama da shekara 20, kuma ya yi waƙoƙi sama da 40 na bege da sauran fannoni na addini duk da kasancewarsa ɗan sanda, sai dai kuma yanzu haka yana fama da larurar cutar mafitsara, inda ya ce, yana buƙatar addu’a daga al`umma masoya Fiyayyen Halitta kan Allah ya kawo sauƙi, ya ba shi lafiya.

Ɗan Sandan Ma`aiki ya shaida ma wakilinmu haka ne jim kaɗan da kamalla wani majalisi da ya gabatar a wani taro da aka yi a fadar mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a ranar Lahadi da ta gabata.

Har ila yau, ya ce daga cikin ƙalubalen da yake fuskanta a halin yanzu shi ne yawan samun kansa a wurare daban-daban musamman kasancewarsa maaikaci a rundunar yansandan Nijeriya wanda wannan yawan canza masa wurin aiki na damunsa musamman kasancewarsa ya na da wannan larura wanda kwanan nan ya baro garin Legas, aka dawo da shi da aiki zuwa makarantar horas da yan`sanda ta Wudil da ke Kano, duk da yake yana godiya ga Allah dangane da walwalar da yake samu a makarantar da samun kulawa daga shugabannin wannan makaranta da ke Wudil.

A ƙarshe ya yaba wa waɗanda suka tallafa masa da kuɗi nan take a lokacin da ya bayyana wa mahalata taron cewa yana buƙatar addu’a amma wasu nan take suka kawo tallafin kuɗi su ka bashi domin ya cigaba da neman lafiya da kuma larurar da yake ciki a yanzu, ta mafitsara wanda har yanzu yana neman cigaba da neman addu’a daga al`umma, a cewar Ɗan Sandan Ma’aiki.

By Editor