Gobara ta kashe mutum biyu a Nijar

Spread the love

Daga BASHIR ISAH

Bayanai daga ƙasar Nijar mai maƙwabtaka da Nijeriya sun ce, mutum biyu sun mutu yayin da wasu sun jikkata sakamakon gobarar da ta tashi a kamfanin SONIDEP da ke birnin Zinder.

Rahotanni na nuni da cewa, iftila’in ya faru ne a ranar Labara a wani wurin ajiyar man fetur na kamfanin da lamarin ya shafa.

Haka nan, an ce gobarar ta ƙone wasu motocin dakon man fetur biyu ƙurmus.

A cewar majiyarmu, gobarar ta tashi ne a daidai lokacin da motocin dakon man suke ƙoƙarin sauke mai a ma’ajin man kamfanin na SONIDEP.

Ta ce gobarar ta haifar da ruɗani da fargaba a cikin zukatan mazauna yankin duk da cewa jami’an tsaro sun killace yankin domin bada kariya ga mutane.

By Editor