Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Hukumar DSS a ranar Laraba a Abuja ta sake gurfanar da Husseni Ismaila, wanda aka fi sani da Maitangaran, wanda ake zargi da hannu wajen kai hare-haren bam a Kano a shekarar 2014, a babban kotun tarayya.
Lokacin da aka kira lamarin, lauyan mai shigar da ƙara, Mista E.A. Aduda, ya shaida wa kotun cewa hukumar ta DSS ta shigar da ƙara ne da gyara tuhume-tuhume huɗu da ake zargin wanda ake ƙara, sannan ya roƙi kotun da ta karanta wa wanda ake ƙara laifin domin ya ɗaukaka ƙara.
“Kai Husseni Ismaila, wanda ake yi wa laqabi da Maitangaran, namiji ɗan shekara 34, ka yi ikirarin cewa shi ɗan ƙungiyar Boko Haram ne, ƙungiyar ta’addanci, don haka ya saɓa wa tanadin dokar rigakafin ta’addanci ta 2013, kuma za a hukunta shi a ƙarƙashin wannan mataki.
“Kai Husseni Ismaila, wanda ake yi wa laƙabi da Maitangaran, namiji ɗan shekara 34 a shekarar 2014, kai tsaye ka shiga aikin ta’addanci kuma ka yi wani saƙo na faifan bidiyo da ya yi ikirarin kai harin bam a babban masallacin Kano.
“Hakan ya kai ga mutuwar ‘yan Nijeriya da dama ciki har da ‘yan sanda. Dokar ta ci karo da sashe na 1 (2) (8) na dokar rigakafin ta’addanci, 2013, kuma ana hukunta shi a ƙarƙashin irin wannan mataki.”
Lauyan da ya shigar da ƙara ya roƙi kotun da ta cigaba da shari’ar bisa la’akari da ƙarar da wanda ake ƙara bai yi ba.
Sai dai Lauyan da ake ƙara, Mista Peter Dajang, ya shaida wa kotun cewa bai kamata a cigaba da shari’ar ba, domin masu gabatar da ƙara sun nuna kwakkwaran umarnin kotu.
A cewar Dajang, kotu a ranar 6 ga watan Disamba, 2021, ta umurci masu gabatar da kara da su mayar da wanda ake tuhuma daga hannunta zuwa gidan gyaran hali na Kuje.
Ya ce, hakan ne ya sa lauyoyinsa da ’yan uwa su samu damar ganawa da shi, amma har yanzu DSS ba ta bi umurnin ba, kasancewar wanda ake tuhuma yana hannun ta.
Ya qara da cewa, masu gabatar da ƙara ba su ɗaukaka ƙara kan hukuncin ba a lokacin da kotu ta bayar, sannan ya ƙara da cewa kotun ba za ta iya zaman ɗaukaka ƙara kan hukuncin da ta yanke ba.
Lauyan wanda ake ƙara ya kuma ƙara da cewa kotun ba ta da hurumin yin watsi da buƙatar masu gabatar da ƙara na sauya hukuncin a kan cewa an yi ta ne a ranar 6 ga watan Disamba, 2021 kuma masu gabatar da ƙara na da kwanaki shida kacal don neman saɓani.
