Tinubu ya yi ganawar sirri da Ganduje da jiga-jigan APC na Kano

Spread the love

Saga MAHDI M. MUHAMMAD

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi ganawar sirri da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje.

Ganduje ya jagoranci wata tawaga da ta kunshi shugabannin jam’iyyar APC reshen Jihar Kano domin ganawa da Tinubu a fadar shugaban qasa ta Aso Rock Villa da ke Abuja, ranar Alhamis.

Taron na ranar Alhamis ya zo ne mako guda bayan da Kotun Koli ta yanke hukuncin amincewa da Abba Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin halastaccen zababben gwamnan jihar da korar karar dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Gawuna.

A watan Maris din da ya gabata ne dai mulki ya sauya sheka daga jam’iyyar APC a lokacin da Gawuna ya samu kuri’u 890,705 inda aka doke shi da kuri’u 1,019,602 bayan hukumar zabe mai zaman kanta ta bayyana Abba Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben.

Sai dai dan takarar na jam’iyyar APC ya fafata da sakamakon zaben a kotu.

Saboda haka, a ranar 17 ga Nuwamba, 2023, Kotun Daukaka Kara ta Abuja ta soke zaben Gwamna Abba Yusuf.

Kotun Daukaka Kara ta amince da hukuncin da Kotun Sauraron Kararrakin Zaben gwamnan Kano ta yanke na soke zaven Yusuf, tare da tabbatar da hukuncin kotun da ta ayyana Gawuna na APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

Yayin da take soke zaven Yusuf, kotun da Mai shari’a Oluyemi Osadebay ke jagoranta ta bayyana cewa 165,663 daga cikin kuri’un sa ba su da inganci.

Bayan kwana biyar, jam’iyyar NNPP ta garzaya ta shigar da kara a gaban Kotun Koli domin kalubalantar hukuncin kotun daukaka kara.

A ranar 12 ga watan Janairu ne Kotun Koli ta mayar da Abba Yusuf a matsayin gwamnan jihar Kano, inda ta soke hukuncin kotun daukaka qara da ta bayyana Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben.

Ba a bayyana ajandar taron na ranar Alhamis ba, kuma wadanda suka halarci taron ba su yi magana da manema labarai na fadar gwamnati ba.

Jam’iyyar NNPP ita ce ta hudu a zaben shugaban kasa da za a yi a watan Fabrairun 2023 a lokacin da ta tsayar da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dakta Rabi’u Kwankwaso.

Ana kallon Kwankwaso a matsayin jigo a jam’iyyar NNPP kuma ya taka rawa wajen ganin Abba Yusuf ya zama gwamna.

By Editor