Fitaccen ɗan bindigan nan Kachalla Bello Turji ya jaddada maganarsa da yayi na cewa, Ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar zamfara ya na bada gudunmuwa sosai wajen ta’addanci a Arewacin Nijeriya.
A wani faifan bidiyo, Turji ya jaddada Matawalle ya kasance yana bada taimakon kuɗi da sauran taimako ga ‘yan ta’adda a yankin Arewacin ƙasar.
Wannan na zuwa ne bayan da Matawallen ya ƙaryata wannan zargin da Turji yayi masa. Ya ce wannan zargin, so a ke a zubar ma Matawalle da mutunci da kuma ɓata mashi suna.
Sai dai wannan na zuwa ne a lokacin da Arewacin Nijeriya ke fama da matsanancin rashin tsaro da kuma zargin da ake cewa wasu manyan yan siyasa na da hannu a cikin ta’azzarar lamarin.
