Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya sanar da cewa gwamnatinsa za ta fara biyan ma’aikata mafi ƙarancin albashi na N85,000.
Sanwo-Olu ya bayyana wannan a daren Laraba yayin wata hira da aka yi da shi a tashar Channels TV, a shirin da aka yi wa take “One on One with Babajide Sanwo-Olu.”
Yayin da aka ambaci batun mafi ƙarancin albashi, gwamnan ya ce: “Ina farin cikin sanar da ku cewa mafi ƙarancin albashi a Legas, wanda muka tattauna tare da ƙungiyarmu, ya zama N85,000 daga yau.
“Ba gasa muke yi ba, don haka ba zan ce muna biyan fiye da wasu ba; abin ya ta’allaƙa ne da irin adadin kuɗin da muke da shi da kuma ƙarfinmu,” in ji gwamnan.
Karin bayani zai biyo baya…
