Gwamna Raɗɗa ya ƙaddamar da wani sahun jami’an community watch corps a Katsina

Spread the love

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta ƙaddamar da ɗauka da horas da kashi na biyu na jami’an community watch corps domin faɗaɗa ayyukan tsaro a faɗin jihar.

A ranar Alhamis da ta gabata ne ƴan ta’adda suka kashe jami’ansu biyar yayin da kuma suka samu raunuka a ƙaramar hukumar Jibiya.

Da ya ke jawabi a wajen bikin yaye jami’an, Gwamna Dikko Raɗɗa, ya ce jami’an za su taimaka wa sauran jami’an tsaro wajen yaƙi da ta’adanci a faɗin jihar.

Ya ce jami’ai 1,466 gwamnatin jihar ta ɗauka aiki shekarar da ta gabata waɗanda su na cigaba da gudanar da aikin samar da tsaro a yankunan da ake fama da rashin tsaro.

Gwamna Raɗɗa ya sanar da cewa su waɗannan sune kashi na biyu da aka ɗauka, kuma za su yi aiki a ƙananan hukumomi 10 da aka gano akwai matsalar tsaro a cikin su.

“Kananan hukumomin sun haɗa da; Dutsinma, Kurfi, Charanchi, Musawa, Kankia, Malumfashi, Ƙafur, Ɗanja, Funtua da Bakori”, inji Raɗɗa.

Ya jinjina wa jami’an tsaron da aka ɗauka a shekarar da ta wuce bisa rawar gani da suka taka wajen samar da tsaro inda a yanzu an samu zaman lafiya a yawancin wuraren da ƴan bindiga suka yi kaka gida.

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar a yankunan da ke fama da rashin tsaro da su taimaka wa jami’an tsaron wajen bada bayanai da zai taimaka wajan gano maɓoyan ƴan ta’adda da ba su bayanan sirri.

By Babaji