Lokaci ya yi domin gyaran dokokin haraji – Idris

Spread the love

Ministan yaɗa labarai Mohammed Idris, ya bayyana cewa haraji wani babbar hanya ce da gwamnati ke samun kuɗaɗe domin samar da ayyukan jin dadin jama’a.

Duk da haka, ya ce tsarin gudanar da haraji a Nijeriya na bukatar gyara, musamman saboda matsalolin da suka shafi tsarawa da aiwatarwa, tare da halayyar masu biyan haraji.

Ministan ya yi nuni da cewa sake duba dokokin haraji da ake yi a yanzu na da muhimmanci, musamman a matsayin wani ɓangare na manufofin farfaɗo da tattalin arziki na ƙasar.

Ya ce cikakkun bayanai kan sabbin ƙudirorin dokokin haraji suna nan a fili, kuma ya yaba wa kwamitin shugaban ƙasa kan gyaran dokokin haraji bisa irin nasarorin da suka samu, musamman wajen haɗa kai da jama’a.

Ya ƙarfafa ‘yan Nijeriya da su yi amfani da damar bayyana ra’ayoyinsu kan sabbin dokokin haraji, tare da bada tabbacin cewa gwamnati za ta saurari koke-koken masu ruwa da tsaki don magance matsalolin da aka taso da su.

Ministan ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu ya jaddada cewa za a yi aiki tare da duk masu ruwa da tsaki don tabbatar da an magance duk wata damuwa.

Shugaban hukumar NIPR, Dr. Ike Neliaku, ya bayyana goyon bayan hukumar ga ƙudirorin dokokin haraji da ke gaban majalisar dokoki. Ya kuma ce hukumar za ta haɗa kai da ma’aikatar domin yaɗa wannan gyara zuwa dukkanin yankunan ƙasa shida na Najeriya. Wannan yana nuni da muhimmancin haɗin kai tsakanin gwamnati da jama’a wajen cimma burin ci gaban ƙasa.

By ukarofi