
Daga BELLO A. BABAJI
Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya ce muhimmanci Birnin Tarayya Abuja ya wuce a bar ta a hannun jam’iyyun ɓangaren adawa.
Ganduje ya faɗi haka ne ranar Alhamis a Abuja a yayin karɓar wasu sababbin mambobin APC da suka sauya sheƙa daga jam’iyyun PDP, LP da wasu.
Shugaban ƙaramar hukumar birni (AMAC), Chris Maikalangu ya jagoranci tawagar a tsohon filin fareti dake Abuja.
Ya ce, hakan ya nuna yadda masu zaɓe suka gamsu da APC a birnin kuma yana fatan za su yi ruwan kuri’u ga jam’iyyar don sake zaɓar Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.
Ya bayyana cewa, bai kamata a bar wa ƴan adawa Abuja ba ganin cewa ita ce cibiyar haɗuwar al’ummar Nijeriya.
Ya kuma ce, daga cikin nasarorin da al’ummar birnin suka samu shine bai wa ƴaƴanta muƙamai a gwamanti da Shugaba Tinubu ya yi, wanda hakan ya ja ra’ayoyi ƴan siyasa shiga APC.
Ya ƙara da cewa, APC ta na cigaba da samun karɓuwa a Abuja da wasu sassan Nijeriya.
