Hukumar zaɓe ta Bauchi za ta yi zaɓen cike gurbin shugaban ƙaramar hukumar Shira

Spread the love

Daga SALIHU ISHAQ MAKERA Bauchi

Hukumar Zaɓe ta Jihar Bauchi (BASIEC), za ta gudanar da zaɓen cike gurbi a ƙaramar hukumar Shira da ke jihar don zaɓen shugaban ƙaramar hukumar da mataimakinsa a ranar 24 ga watan Mayu, 2025.
Shugaban hukumar BASIEC Alhaji Ahmed Makama ne ya bayyana haka a hirarsa da manema labarai a ofishinsa da ke Bauchi a yammacin ranar Alhamis da ta gabata.
Alhaji Ahmed Makama ya bayyana cewa an samu gurbin shugaban ƙaramar hukumar da mataimakinsa ne saboda kansilolinsu sun tsige su a kwanakin baya.
Hukumar ta ce bisa dokar zaɓe ta 2008 za a fara kamfen na neman muƙaman biyu tun daga ranar ranar Alhamis 8 ga Mayun nan.
Shugaban ya ce duk mai son tsayawa takarar shugaban ƙaramar hukumar zai yanki fom a kan Naira miliyan ɗaya mataimakin shugaba kuma a kan Naira 500,000.
Hukumar ta ce za ta zauna da jami’yyun siyasa da shugabannin hukumomin taro da masu ruwa-da-tsaki kan zaɓen a wannan mako a ofishinta na Shira.
Ya ce, yayin da jam’iyyu za su gudanar da zaɓuɓɓukan fitar da ‘yan takara, hukumar a nata ɓangaren za ta horar da malaman zaɓe da masu duba yadda za a gudanar da zaɓen da sauran shirye-shiryen zaɓen.
Shugaban ya ce za a raba kayan yin zaɓe Kuma a ranar za a ana gobe zaɓen kuma a kawo ƙarshen kamfe ranar 23 ga Mayu washe gari 24 ga watan a gudanar da zaɓen.
Alhaji Ahmed Makama ya ce an shirya ingantaccen zaɓe da kowa zai gamsu.
Alhaji Ahmed ya buƙaci al’ummar yankin da jam’iyyun siyasa da sauran masu ruwa-da-tsaki su taimaka wajen gudanar da zaɓen cikin nasara da kwanciyar hankali.

By ukarofi