
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Hukumar Hana yi wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Ta’annati EFCC, ta ayyana sirikin tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar kuma ɗan kasuwa, wato Abdullahi Bashir Haske a matsayin wanda ake nema ruwa-a-jallo bisa zargin sa da hannun a badaƙalar wasu kuɗaɗe.
Kakakin hukumar, Dele Oyewale ya bayyana hakan a wata takarda da aka sanya a allon sanarwar ofishinsu, ranar Alhamis.
A cewar EFCC, Haske mai shekaru 38 yana da hannu a kitsa makircin babban laifi da kuma sauya akalar wasu kuɗaɗe.
Don haka hukumar ta wallafa hotonsa a takardar da sunan tana nemansa ruwa-a-jallo.
Ta ce, ganin sa na ƙarshe shi ne wanda aka yi a No. 6 hanyar Mosley da ke yankin Ikoyi da layin Idejo da ke Victoria Island a jihar Legas.
Akan haka ta yi kira ga ƴan Nijeriya du su taimaka mata da rahoton zirga-zirgarsa ta hanyar sanar da kowane ɗaya daga cikin ofisoshinta a ƙasar.
Daga cikin su akwai na Abuja, Lagas, Fatakwal, Kano, Ibadan, Enugu, Ilorin, Kaduna, Sakkwato, Maiduguri, Benin, Makurɗi, Uyo, da kuma Gombe.
