
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Wasu ababen fashewa guda biyu sun tarwatse a birnin Damascus, inda Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya halarci wani zama a ranar Talata yayin da ya kai ziyara Siriya.
A cewar Reuters, fashe-fashen sun faru ne a kusa da otal ɗin su Macron da ke babban birnin ƙasar, lamarin da ya tilasta wa hukumomin tsaro rufe hanyoyin zuwa yankin da ƙarfafa matakan tsaro.
An ruwaito cewa, boma-boman sun fashe ne a wajen taruwar jama’a da ke tsakanin ma’aikatar walwalar Siriya da gidan adana kayan tarihi a sassan yankin da Macron ya gana da ƙungiyoyin al’umma.
Kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ruwaito cewa kimanin mutane 18 ne suka jikkata a sakamakon faruwar al’amarin ciki har da jami’an ‘yan sanda huɗu.
Haka kuma, an ga yadda hayaƙi ya ɗumama wajen, yayin da jami’an agajin gaggawa suka yi ƙoƙarin shawo kan al’amarin.
