Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe
Ƙungiyar Civil Society Action Coalition on Education for All (CSACEFA) reshen Jihar Gombe, ta yaba wa Gidauniyar ci gaban al’umma ta Misilli bisa ƙoƙarin da take yi wajen shigar da yaran da ba sa zuwa makaranta cikin tsarin karatu.
Mai kula da CSACEFA a jihar, Hajiya Halima Ahmed Mahdi, ta bayyana hakan a wata hira da wakilinmu a Gombe, yayin bikin cika shekaru huɗu da kafuwar gidauniyar da aka gudanar a unguwar Dawaki.
Mahdi ta ce ayyukan gidauniyar na taimakawa wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, musamman waɗanda suka fito daga iyalai masu ƙaramin ƙarfi.
Ta ce shigar da yara makaranta, samar da kayan karatu, bayar da tallafin karatu da jagoranci na daga cikin muhimman hanyoyin da za su taimaka wajen magance matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta.
“Ilimi shi ne ginshiƙin kowace al’umma. Don haka muna yaba wa daidaikun mutane da ƙungiyoyin da ke taimakawa wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta ta hanyar shigar da su makarantu, samar da kayan karatu, tallafin karatu da jagoranci,” in ji Mahdi.
Ta kuma yaba wa Isma’ila Uba Misilli bisa tallafa wa shigar da yara makarantu, tana mai bayyana hakan a matsayin muhimmiyar gudunmawa ga ci gaban ilimi a jihar.
Mahdi ta yi kira ga sauran masu hannu da shuni, ƙungiyoyi da kungiyoyin agaji da su yi koyi da gidauniyar wajen zuba jari a harkar ilimi da tallafa wa yara daga iyalai marasa galihu.
Ta ce magance matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta na buƙatar haɗin gwiwar gwamnati, iyaye, malamai, al’umma, ƙungiyoyin farar hula da kamfanoni masu zaman kansu.
A wani ɓangare na bayaninta, Mahdi ta bayyana cewa CSACEFA ta gudanar da zaɓen sabbin shugabanninta a ranar 10 ga Satumba, 2026, inda dukkan mukamai biyar suka koma hannun waɗanda suka tsaya takara ba tare da hamayya ba.
Ta ce an sake zaɓenta a matsayin Mai Kula da CSACEFA a jihar, yayin da Barde Salihu ya zama Sakatare; Abubakar Umar Aliyu ya zama Provost; Pononyamba Ishaku Garba ya zama Ma’aji; sannan Adamu Alhaji Abubakar ya zama Jami’in Hulɗa da Jama’a.
Mahdi ta ce sabbin shugabannin za su ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki wajen inganta ilimi da samar da dama ga yara a faɗin jihar.
Ta kuma yi kira da a ƙara mayar da hankali kan ilimin zaman lafiya, musamman tsakanin yara da matasa, tana mai cewa koyar da haƙuri, tattaunawa da mutunta juna zai taimaka wajen gina al’umma mai zaman lafiya da ci gaba.
