A Daura za a yi jana’izar Buhari – Raɗɗa

Spread the love

Daga UMAR GARBA a Katsina

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Raɗɗa, ya bayyana cewa za a yi jana’izar tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, a mahaifarsa dake Daura, Jihar Katsina.

Wannan na zuwa ne yayin da aka tabbatar da rasuwar tsohon shugaban ƙasar a birnin Landan.

Gwamna Raɗɗa, wanda yanzu haka ke ƙasar Ingila, ya tabbatar wa da DW Hausa cewa ana ci gaba da shirye-shirye domin kawo gawar tsohon shugaban ƙasar gida domin gudanar da jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

By ukarofi