Alhaji Abu Ɗanmalam Karofi ya rasu a Katsina

Spread the love

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina

Tsohon babban sakatare kuma raya karkaran Katsina, Alhaji Abu Ɗanmalam Karofi ya rasu bayan yayi fama da doguwar rashin lafiya a Katsina.

Ɗanmalam Karofi wanda aka fi sani da ADK shi ke kula da ƙananan hukumomin jihar a lokacin Marigayi Umaru Musa Yar’adua na gwamnan jihar.

Marigayi ADK za a riƙa tunawa da shi wajen jajircewa na ganin shugabannin ƙananan hukumomi dole su gaskiya da riƙon amana wajen tafiyar da mulkin ƙananan hukumomin jihar.

Haka kuma an bayyana Karofi a matsayin mai gaskiya da jajircewa wajen ganin shugabannin ƙananan hukumomi sun sarrafa kason kuɗaɗen su yadda ya dace.

An yi jana’izar sa a mahaifarsa da ke Rayuka a cikin garin Katsina.

By ukarofi

Leave a Reply