
Daga BELLO A. BABAJI
Shugaba Bola Tinubu ya amince da ware Naira biliyan 2 domin sake gina baki ɗaya gidajen da ambaliyar Mokwa a Jihar Neja ta lalata.
Mataimakinsa, Kashim Shettima ne ya faɗi hakan a yayin ziyarasa a garin Mokwa a yau Laraba, biyo bayan ambaliyar da ta yi sanadin rasa rayuka da dukiyoyi dama tare da ɗaiɗaita ɗaruruwan mutane.
Shettima ya kuma ce, Shugaban ƙasar ya umarci a gaggauta kai tireloli 20 na shinkafa ga mutanen da iftila’in ya afka wa a ƙoƙarin gwamnatinsa na rage musu raďaďi.
Ya tabbatar musu da cewa, Shugaba Tinubu na tare da su a yayin jimamin al’amarin, sannan za a warware dukkan matsalolin da ke damun su.
Har’ilayau, ya ce Tinubu ya umarci a gaggauta gyara gadoji da magudanan ruwa da suka lalace a waurare da ambaliyar ta shafa.
Tuni dai jami’an gwamnati suke aikin bincike da ceto waɗanda suka ɓata a sanadiyyar ambaliyar, wadda ta yi dalilin tarwatsa gidaje da rasa rayukan sama da mazauna guda 200 a yayin da ta auku a ranar 28 ga Mayu, 2025.

