Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da iyalan fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na Nijeriya, Sheikh (Dr.) Bashir Ahmad Sakkwato.
Harin ya faru ne a lokacin da matar malamin, ’ya’yansa biyu, mahaifiyarsa da ’yar uwarsa suke tafiya tare. Abin takaici, an kashe direban motarsu a harin kwanton ɓaunar.
Dokta Bashir Sokoto, wanda ya yi fice wajen bayar da gudunmawarsa ga koyarwar addinin Musulunci da kuma tasirinsa a cikin al’ummar Musulmi, malami ne da ake girmamawa sosai a Nijeriya.
Sace iyalan nasa da aka yi ya jefa fargaba a sassan yankin, inda da yawa ke nuna damuwarsu ga lafiyar iyalansa tare da yin Allah-wadai da ƙaruwar rashin tsaro a aasar.
’Yan ta’addan da ke zaman wani ɓangare na barazana a arewacin Nijeriya, sun kai harin ne a wata hanyar da ba a bayyana ba a lokacin da iyalan ke tafiya.
Har yanzu dai hukumomi ba su tabbatar da wani buƙatu na neman kuzin fansa ba, amma ana alaƙanta garkuwa irin wannan da neman kuɗin fansa.
Shugabanin yankin da ’yan uwa da ƙungiyoyin addinai sun yi kira ga gwamnati da ta ƙara zage damtse wajen ganin an kuɓutar da iyalan da aka sace tare da gurfanar da waɗanda suka aikata laifin a gaban kotu.
Sace iyalan da aka yi ya ƙara nuna taɓarɓarewar yanayin tsaro a arewacin Nijeriya, inda matsalar fashi da garkuwa da mutane ya zama ruwan dare.
Dr. Bashir, wanda koyarwarsa ta ta’allaƙa ne kan zaman lafiya, adalci da zamantakewar addini, har yanzu bai fitar da wata sanarwa ba dangane da lamarin.
Jama’a na jiran ƙarin bayani yayin da ake kyautata zaton jami’an tsaro na aara zage damtse wajen zaƙulo masu garkuwa da mutanen.
