Bankin AfDB zai samar da guraben aiki miliyan 25 zuwa shekarar 2025

Daga AMINA YUSUF ALI

Bankin cigaban Afirka  (AfDB) ya bayyaana cewa, yanzu haka Bankin yana da aniyar samar da guraben ayyukan yi guda miliyan 25, kafin nan kafin shekarar 2025, a Nijeriya. 

Hukumar rukunin bankunan na ƙoƙarin tabbatar da hakan ne ta hanyar zuba hannayen jari masu gwaɓi a masana’antun fasahar zamani na ƙasar nan. Tare da haɗa hannu da wasu kamfanonin don samun guraben ayyuka barkatai a Nijeriya. 

Wannan bayanai sun fito ne daga bakin shugaban rukunan AfDB, Dakta Akinwunmi Adesina a ranar Juma’ar da ta gabata. A yayin da yake gabatar da lakca a kan yadda shafukan yanar gizo da tsaron ƙasa da kuma sauye-sauyen rayuwa da za su iya kawo daidaito a Afirka. An gudanar da taron a jihar Legas. 

A cewar sa, Nijeriya tana da damarmaki da yawa waɗanda ƙasashen Duniya suke da buƙatar su ma su shigo a dama da su, wajen zuba jari da kasuwanci. 

Ya ƙara da cewa, a yanzu haka, AfDB ya shirya tsaf, don tallafa wa Nijeriya. Inda nan ba da daɗewa ba, za su zuba hannun jarin Dala miliyan ɗari biyar a sassan fasahar zamani da kasuwanci a ƙasar.

Wanda suke sa ran shigowar wasu ƙasashen domin su ma su ba da tasu gudunmowsr don a haɗa gwiwa a cimma manufar da aka nufa.