Bayan Azahar za a yi jana’izar Attahiru

Spread the love

Daga AISHA ASAS

Kawo yanzu, jama’a da dama na tsumayar jana’izar Babban Hafsan Sojoji, Ibrahim Attahiru, wanda za a gudanar a babban Masallacin Abuja.

Manyan jami’an soja 6 ne za a yi wa Sallar Jana’izar waɗanda suka rasu sakamakon hadarin jirgin sama da ya rutsa da su a Kaduna.

Yayin da ragowan sojojin za a binne su ne daidai da tsarin addininsu na Kirista.

By Editor