Cutar Kwalara ta hallaka mutum 13 a jihar Neja

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Cutar amai da gudawa wato Kwalara ta ɓulla a ƙananan hukumomi shida a jihar Neja, inda ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 13, yayin da sama da 236 suna jinya a asibiti.

An fara samun rahoton ɓullar cutar ne a ƙaramar hukumar Shiroro, amma yanzu ta bazu zuwa Bosso da Minna da Magama Bida da kuma Munya.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa kwamishinan kiwon lafiya a matakin farko, Dr. Ibrahim Dangana ne ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa gwamnati ta ɗauki matakai daban-daban don daƙile yaɗuwar cutar.

“Mun kafa wuraren keɓance marasa lafiya a kowanne daga cikin yankunan da abin ya shafa,” inji kwamishinan.

Ya kuma ce ana gudanar da wayar da kai ga jama’a kan cutar da yadda za a kiyaye ta hannun ƙungiyoyin addini da masarautu takwas na jihar.

Gwamnatin jihar ta kuma buɗe wuraren keɓance marasa lafiya a tsohuwar asibitin Idris Ibrahim Kuta da ke Minna.

Daraktan lafiyar jama’a, Dr. Ibrahim Idris, ya tabbatar da cewa Minna da Bosso da Shiroro sune wuraren da cutar ta fi ƙamari.

By ukarofi