Wani jirgin sama mai saukar ungulu da ba a kai ga tantancewa ba ya yi hatsari a yankin Oba Akran Ikeja a Jihar Legas.
An ce jirgin ya faɗa wani gini ne kana daga bisani ya kama da wuta a wannan Talatar.
Majiyarmu ta ce an samu ceto mutum huɗu da ke cikin jirgin da ransu in ji wani jami’in hukumar NEMA.
Ya zuwa haɗa wannan labari ba a kai ga gano dalilin aukuwar hatsarin ba.