Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta tabbatar da Adeleke a matsayin Gwamnan Osun

Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar da Adegboyega Oyetola na Jam’iyyar APC ya ɗaukaka inda yake ƙalubalantar nasarar da Ademola Adeleke na Jam’iyyar PDP ya samu a matsayin Gwamnan Jihar Osun.

Da yake karanto hukuncin yayin zaman kotun a ranar Talata, Mai Shari’a Emmanuel Agim ya tabbatar da hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke na cewa Adeleke shi ne wanda ya yi nasara a zaɓen na Osun.

Kotun Ƙolin ta ce mai ƙara ya gaza gabatar wa kotun gamsassun hujjoji kan zargin da ya yi cewa an zuba ƙuri’a wuce kima a zaɓen gwamnan jihar Osun da ya gudana ran 16 ga Yulin 2022.

Don haka duka alƙalan da ke sauraren shari’ar su biyar suka tabbatar da nasarar Adeleke.